| Hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
Sakon Shugaba Tinubu na Sabuwar Shekara: Za a tallafa wa mutum 1,000 a kowace mazaɓa a Nijeriya
Shugaban na Nijeriya ya kuma bayyana cewa za a haɓaka tattalin arzikin 'yan ƙasar ta hanyar bunƙasa harkokin noma, da cinikayya da sarrafa abinci da hakar ma’adinai.
Sakon Shugaba Tinubu na Sabuwar Shekara: Za a tallafa wa mutum 1,000 a kowace mazaɓa a Nijeriya
Shugaba Tinubu ya fitar da wallafa saƙon na sabuwar shekarar 2026 a shafinsa na X ranar 1 ga Janairun 2026 / Nigeria Presidency
1 Janairu 2026

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya sha alwashin bunƙasa shirin tallafa wa aƙalla mutum miliyan 10 a Nijeriya ta yadda za su bunƙasa harkar tattalin arzikinsu da rage talauci a ƙasar.

Tinubu ya bayyana haka ne a cikin saƙonsa na sabuwar shekarar 2025 ga ‘yan ƙasar.

“Za mu inganta aiwatar da Shirin Bunƙasa Unguwanni da ke cikin Shirin Farfado da Fata (Renewed Hope), inda muke fatan sanya akalla ‘yan Nijeriya miliyan 10 cikin harkokin tattalin arziki, ta hanyar tallafa wa akalla mutum 1,000 a kowace mazaɓa a duka mazaɓu 8,809 a faɗin ƙasar,” in ji shugaba Tinubu a cikin sakon.

Masu AlakaTRT Afrika - Hotuna: Wasan tartsatsin wuta da sauran bukukuwa na maraba da Sabuwar Shekara ta 2026

Shugaban na Nijeriya ya kuma bayyana cewa za a habaka tattalin arzikin mutane ta hanyar bunkasa harkokin noma, da cinikayya da sarrafa abinci da hakar ma’adinai.

Tsaro da zaman lafiya

Shugaban Bola Tinubu ya bayyana cewa jami’an tsaro Nijeriya na ci gaba da matsa wa ‘yanta’adda da masu kai hare-hare lamba, musamman a yankin arewacin kasar.

Ya bayyana cewa tun bayan harin da Amurka ta kai a yankin arewa maso yammacin Nijeriya da hadin gwiwar gwamnati, sojoji sun zafafa hare-hare a kan kungiyoyin ta’adda da dabobin miyagu a arewa maso gabas da arewa maso yamma.

Ya ce “A 2026, jami’an tsaronmu da jami’an leken asirinmu za su karfafa hadaka da abokan huldarmu na nahiya da na duniya, don kawar da duk wata barazana ga tsaron kasarmu.”

A cewar shugaban yana da iminin cewa bai wa jihohi damar samar da ‘yansandansu tare da yin aiki yadda ya kamata “abu ne mai muhimmanci wajen magance matsalar ta’addanci, da harkar satar mutane da sauran matsalolin tsaro masu alaka da su.”

Sakon na shugaba Tinubu ya kuma kunshi bayanai kan nasarar da Nijeriya ta samu a 2025 a fannin tattalin arziki da suka hada da raguwar hauhawar farashin kayayyaki da bunkasar ma’aunin tattalin arziki na GDP, da tagomashin kasuwar hannun jari ta Nijeriya inda ta bunƙasa da kaso 48.12 cikin dari.

Sannan ya yi alkawarin cewa, gwamnati ta sha alwashin ci gaba da rage hauhawar farashi a 2026 don amfanin duka ‘yan kasa.

Rumbun Labarai
Fiye da mutum 50 ne suka mutu a harin 'yan bindiga a jihar Neja ta tsakiyar Nijeriya
‘Yansandan Nijeriya sun gayyaci Fasto Chris Okafor bisa zarge-zargen aikata fyaɗe
Nijeriya ta kama Indiyawa 22 bisa zargin shigar da hodar ibilis ƙasar
Aƙalla mutane 25 sun mutu, an ceto 13 a hatsarin kwale-kwale a Jihar Yobe ta Nijeriya
An kashe fiye da mutum 30, an sace wasu da dama a Jihar Niger a tsakiyar Nijeriya: 'yansanda
Sojojin Nijeirya sun gano albarusai masu yawa a cikin kwata a Maiduguri
Abin da bincike ya gano na musabbabin annobar cutar ƙoda a Jihar Yobe
Rundunar sojin Nijeriya ta kashe ‘yan ta’adda 47 a farmaki da ta kai a faɗin ƙasar
Gobara ta ƙona Masallacin Shitta-Bey da ke Lagos wanda ke da alaƙa da Daular Usmaniyya ta Turkiyya
Kotu ta ba da umarnin tsare Abubakar Malami da ɗansa a gidan yarin Kuje
Wani abu ya fashe a Babban Asibiti a Jihar Kebbi ta Nijeriya
‘Yan jarida bakwai sun mutu sakamakon hatsarin mota a Gombe
Siyasar Kano: Shin Kwankwaso ne zai tura Gwamna Abba  Jam'iyyar APC ko kuwa gaban kansa yake son yi?
Shugaba Tinubu ya tafi Turai don ci gaba da hutun ƙarshen shekara
Bam da aka binne a titi ya halaka mutane a Jihar Zamfara, wasu da dama sun jikkata
Mun tuntuɓi Turkiyya domin neman agaji kan matsalar tsaro – Shugaban Nijeriya Tinubu
Hare-haren Amurka sun sauka a wuraren da babu 'yan ƙungiyar Daesh a Sokoto, in ji mazauna yankin
Jirgin Saman Sojin Nijeriya C-130 da aka tsare a Burkina Faso ya isa Portugal domin yin gyara
Da haɗin gwiwarmu Amurka ta kai hari Nijeriya: Ma'aikatar Harkokin Waje
Amurka ta kai hari kan mayaƙan Daesh a Nijeriya, in ji Donald Trump