| Hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
Fiye da mutum 50 ne suka mutu a harin 'yan bindiga a jihar Neja ta tsakiyar Nijeriya
Rahotanni daga yankin sun ce adadin wadanda suka mutu sakamakon harin da aka kai a wata kasuwa a jihar Neja ta Nijeriya ya haura 50.
Fiye da mutum 50 ne suka mutu a harin 'yan bindiga a jihar Neja ta tsakiyar Nijeriya
'Yan bindiga sun addabi jihar Neja da ke tsakiyar Nijeriya. / Others
5 Janairu 2026

‘Yan bindiga dauke da makamai ne suka kai hari kan Kasuwar Daji a kauyen Demo na jihar Neja inda suka kashe fiye da mutane 50 tare da yin garkuwa da wasu da dama, in ji mazauna yankin.

Wasu 'yan bindiga dauke da makamai sun kai hari Kasuwar Daji da ke kauyen Demo a ranar Asabar, inda suka bude wuta ga mazauna yankin ba tare da wani dalili ba, suka sace mutane da dama tare da sace kayan abinci.

An yi jana'izar jama'a da yawa da suka mutu yayin da aka kai wadanda suka jikkata zuwa asbiti.

Shugaba Bola Tinubu ya yi Allah wadai da harin kuma ya umarci jami'an tsaro da su kama wadanda suka aikata laifin.

"Suna jarraba jajircewar kasarmu kuma dole ne su fuskanci sakamakon laifukan da suka aikata," in ji shi.

Tinubu ya kuma umarci hukumomi da su gaggauta ceto duk mutanen da aka sace a lokacin harin.

Jihar Neja ta sha fuskantar hare-haren ta'addanci akai-akai a cikin 'yan makonnin nan, musamman a yankunan karkara da ke fuskantar barazanar kungiyoyi masu dauke da makamai da ke aiki daga cikin dazuzzuka.

A ranar 21 ga Nuwamban bara, 'yan bindiga dauke da makamai sun sace mutane 315 -- da suka hada da dalibai 303 da malamai 12 -- daga makarantar Firamare da Sakandare ta Katolika ta St. Mary da ke Papiri, karamar Hukumar Agwara.

Yayin da kimanin dalibai 50 suka tsere a ranar da aka kai harin, gwamnatin tarayya daga baya ta tabbatar da sakin wasu su 100.

A ranar 21 ga Disamba, Ministan Watsa Labarai Mohammed Idris ya sanar da cewa an kubutar da dukkan sauran daliban da aka sace.

Rumbun Labarai
‘Yansandan Nijeriya sun gayyaci Fasto Chris Okafor bisa zarge-zargen aikata fyaɗe
Nijeriya ta kama Indiyawa 22 bisa zargin shigar da hodar ibilis ƙasar
Aƙalla mutane 25 sun mutu, an ceto 13 a hatsarin kwale-kwale a Jihar Yobe ta Nijeriya
An kashe fiye da mutum 30, an sace wasu da dama a Jihar Niger a tsakiyar Nijeriya: 'yansanda
Sojojin Nijeirya sun gano albarusai masu yawa a cikin kwata a Maiduguri
Sakon Shugaba Tinubu na Sabuwar Shekara: Za a tallafa wa mutum 1,000 a kowace mazaɓa a Nijeriya
Abin da bincike ya gano na musabbabin annobar cutar ƙoda a Jihar Yobe
Rundunar sojin Nijeriya ta kashe ‘yan ta’adda 47 a farmaki da ta kai a faɗin ƙasar
Gobara ta ƙona Masallacin Shitta-Bey da ke Lagos wanda ke da alaƙa da Daular Usmaniyya ta Turkiyya
Kotu ta ba da umarnin tsare Abubakar Malami da ɗansa a gidan yarin Kuje
Wani abu ya fashe a Babban Asibiti a Jihar Kebbi ta Nijeriya
‘Yan jarida bakwai sun mutu sakamakon hatsarin mota a Gombe
Siyasar Kano: Shin Kwankwaso ne zai tura Gwamna Abba  Jam'iyyar APC ko kuwa gaban kansa yake son yi?
Shugaba Tinubu ya tafi Turai don ci gaba da hutun ƙarshen shekara
Bam da aka binne a titi ya halaka mutane a Jihar Zamfara, wasu da dama sun jikkata
Mun tuntuɓi Turkiyya domin neman agaji kan matsalar tsaro – Shugaban Nijeriya Tinubu
Hare-haren Amurka sun sauka a wuraren da babu 'yan ƙungiyar Daesh a Sokoto, in ji mazauna yankin
Jirgin Saman Sojin Nijeriya C-130 da aka tsare a Burkina Faso ya isa Portugal domin yin gyara
Da haɗin gwiwarmu Amurka ta kai hari Nijeriya: Ma'aikatar Harkokin Waje
Amurka ta kai hari kan mayaƙan Daesh a Nijeriya, in ji Donald Trump