| Hausa
NIJERIYA
1 minti karatu
Nijeriya ta kama Indiyawa 22 bisa zargin shigar da hodar ibilis ƙasar
An jima ana yi wa Nijeriya kallon wata cibiyar samarwa da safarar miyagun kwayoyi da aka nufi kai su Turai da sauran kasashen Afirka.
Nijeriya ta kama Indiyawa 22 bisa zargin shigar da hodar ibilis ƙasar
Jirgin ruwan da ya yi safara cocaine wanda ya taso daga Tsibirin Marshall zuwa Nijeriya / NDLEA
4 Janairu 2026

Hukumar Yaƙi da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ta Nijeriya NDLEA ta ce ta kama ma’aikatan jirgin ruwa Indiyawa 22 bayan an gano hodar ibilis, wato cocaine mai nauyin kilogirm 31.5 a cikin jirgin, a gaɓar ruwan Legas.

An yi kamen ne a ranar 2 ga Janairu a wani jirgin ruwa mai suna MV Aruna Hulya “wanda ya taso daga Tsibirin Marshall,” a cewar wata sanarwa da Kakakin na NDLEA Femi Babafemi ya fitar ranar Lahadi.

An jima ana yi wa Nijeriya kallon wata cibiyar samarwa da safarar miyagun kwayoyi da aka nufi kai su Turai da sauran kasashen Afirka.

A watan Nuwamba NDLEA ta ce ta kama ‘yan Philippines su 20 a cikin jirgin ruwa ɗauke da aƙalla kilogiram 20 na cocaine da suka yi safararta daga Brazil sannan suka nufi gaɓar ruwa ta Same.

Tun da farko a cikin watan kuma, hukumar ta ce tana aiki da hukumoin yaƙi da shan miyagun ƙwayoyi na Amurka da Birtaniya wajen bincika wasu gungun mutane da suka shigar da cocaine mai nauyin kilogiram 1,000 da aka gano a cikin wata kwantena a gaɓar ruwan Legas.

Rumbun Labarai
Fiye da mutum 50 ne suka mutu a harin 'yan bindiga a jihar Neja ta tsakiyar Nijeriya
‘Yansandan Nijeriya sun gayyaci Fasto Chris Okafor bisa zarge-zargen aikata fyaɗe
Aƙalla mutane 25 sun mutu, an ceto 13 a hatsarin kwale-kwale a Jihar Yobe ta Nijeriya
An kashe fiye da mutum 30, an sace wasu da dama a Jihar Niger a tsakiyar Nijeriya: 'yansanda
Sojojin Nijeirya sun gano albarusai masu yawa a cikin kwata a Maiduguri
Sakon Shugaba Tinubu na Sabuwar Shekara: Za a tallafa wa mutum 1,000 a kowace mazaɓa a Nijeriya
Abin da bincike ya gano na musabbabin annobar cutar ƙoda a Jihar Yobe
Rundunar sojin Nijeriya ta kashe ‘yan ta’adda 47 a farmaki da ta kai a faɗin ƙasar
Gobara ta ƙona Masallacin Shitta-Bey da ke Lagos wanda ke da alaƙa da Daular Usmaniyya ta Turkiyya
Kotu ta ba da umarnin tsare Abubakar Malami da ɗansa a gidan yarin Kuje
Wani abu ya fashe a Babban Asibiti a Jihar Kebbi ta Nijeriya
‘Yan jarida bakwai sun mutu sakamakon hatsarin mota a Gombe
Siyasar Kano: Shin Kwankwaso ne zai tura Gwamna Abba  Jam'iyyar APC ko kuwa gaban kansa yake son yi?
Shugaba Tinubu ya tafi Turai don ci gaba da hutun ƙarshen shekara
Bam da aka binne a titi ya halaka mutane a Jihar Zamfara, wasu da dama sun jikkata
Mun tuntuɓi Turkiyya domin neman agaji kan matsalar tsaro – Shugaban Nijeriya Tinubu
Hare-haren Amurka sun sauka a wuraren da babu 'yan ƙungiyar Daesh a Sokoto, in ji mazauna yankin
Jirgin Saman Sojin Nijeriya C-130 da aka tsare a Burkina Faso ya isa Portugal domin yin gyara
Da haɗin gwiwarmu Amurka ta kai hari Nijeriya: Ma'aikatar Harkokin Waje
Amurka ta kai hari kan mayaƙan Daesh a Nijeriya, in ji Donald Trump