| Hausa
NIJERIYA
1 minti karatu
An kashe fiye da mutum 30, an sace wasu da dama a Jihar Niger a tsakiyar Nijeriya: 'yansanda
Mahara sun kashe fiye da mutum 30 sun kuma sace wasu da dama a jihar Neja ta arewa ta tsakiyar Nijeriya, kamar yadda 'yansanda suka bayyyana a ranar Lahadi.
An kashe fiye da mutum 30, an sace wasu da dama a Jihar Niger a tsakiyar Nijeriya: 'yansanda
At least 30 people have been killed in Nigeria's central state of Niger, police said on January 3, 2026. / Reuters
4 Janairu 2026

Fiye da mutane 30 aka kashe, aka sace wasu da dama a wani hari da 'yan fashin' daji suka kai a Jihar Neja ta tsakiyar Najeriya, in ji 'yan sanda a ranar Lahadi.

Maharan sun kutsa kauyen Kasuwan Daji a karamar hukumar Kabe, suka ƙone kasuwa kafin su kwashe kayan shaguna domin neman abinci.

"Fiye da mutane 30 ne suka rasa rayukansu yayin harin, wasu mutanen kuma an sace su," a lokacin fashin ranar Asabar, in ji Wasiu Abiodun, kakakin 'yan sandan Neja.

Gungun masu satar mutane, wadanda mazauna ke kiran su 'yan fashin daji, suna yawan sace jama'a don neman kudin fansa da kuma fashi a ƙauyuka a wasu sassan arewa maso yamma da arewa ta tsakiyar Najeriya.

Wajen da matsalar ta yi ƙamari

Jihar Niger ta kasance ɗaya daga cikin jihohin da suka fi fuskantar wannan matsalar a 'yan watannin da suka gabata.

A watan Nuwamba, wasu gungun ‘yan bindiga sun sace fiye da ɗalibai 250 da ma'aikata daga wata makaranta a jihar.

Hukumomi sun sanar da sakin su makonni bayan satar.

Gwamnatin Najeriya ta ƙara ƙoƙarin inganta tsaro bayan jerin sace-sacen. Yawancin wadanda aka sace kwanan nan an riga an ceto su.

Rumbun Labarai
Fiye da mutum 50 ne suka mutu a harin 'yan bindiga a jihar Neja ta tsakiyar Nijeriya
‘Yansandan Nijeriya sun gayyaci Fasto Chris Okafor bisa zarge-zargen aikata fyaɗe
Nijeriya ta kama Indiyawa 22 bisa zargin shigar da hodar ibilis ƙasar
Aƙalla mutane 25 sun mutu, an ceto 13 a hatsarin kwale-kwale a Jihar Yobe ta Nijeriya
Sojojin Nijeirya sun gano albarusai masu yawa a cikin kwata a Maiduguri
Sakon Shugaba Tinubu na Sabuwar Shekara: Za a tallafa wa mutum 1,000 a kowace mazaɓa a Nijeriya
Abin da bincike ya gano na musabbabin annobar cutar ƙoda a Jihar Yobe
Rundunar sojin Nijeriya ta kashe ‘yan ta’adda 47 a farmaki da ta kai a faɗin ƙasar
Gobara ta ƙona Masallacin Shitta-Bey da ke Lagos wanda ke da alaƙa da Daular Usmaniyya ta Turkiyya
Kotu ta ba da umarnin tsare Abubakar Malami da ɗansa a gidan yarin Kuje
Wani abu ya fashe a Babban Asibiti a Jihar Kebbi ta Nijeriya
‘Yan jarida bakwai sun mutu sakamakon hatsarin mota a Gombe
Siyasar Kano: Shin Kwankwaso ne zai tura Gwamna Abba  Jam'iyyar APC ko kuwa gaban kansa yake son yi?
Shugaba Tinubu ya tafi Turai don ci gaba da hutun ƙarshen shekara
Bam da aka binne a titi ya halaka mutane a Jihar Zamfara, wasu da dama sun jikkata
Mun tuntuɓi Turkiyya domin neman agaji kan matsalar tsaro – Shugaban Nijeriya Tinubu
Hare-haren Amurka sun sauka a wuraren da babu 'yan ƙungiyar Daesh a Sokoto, in ji mazauna yankin
Jirgin Saman Sojin Nijeriya C-130 da aka tsare a Burkina Faso ya isa Portugal domin yin gyara
Da haɗin gwiwarmu Amurka ta kai hari Nijeriya: Ma'aikatar Harkokin Waje
Amurka ta kai hari kan mayaƙan Daesh a Nijeriya, in ji Donald Trump