AFIRKA
2 minti karatu
Sojojin Sudan sun harbo jirgi maras matuƙi na RSF a Kordofan ta Arewa
Sojojin sun kakkaɓo jirgi maras matuƙin samfarin ƙasar China a lokacin da yake wucewa ta saman birnin inda rahotanni suka ce jirgin ya nufi yammacin El-Obeid domin kai hari kan wuraren soja da na farar-hula
Sojojin Sudan sun harbo jirgi maras matuƙi na RSF a Kordofan ta Arewa
Wannan rikici na Sudan ya yi sanadiyyar mutuwar dubban mutane da kuma tilasta wa miliyoyin mutane guduwa daga gidajensu.
10 awanni baya

Sojojin Sudan sun harbo jirgin sama maras matuƙi da dakarun RSF suke sarrafawa a birnin El-Obeid a Jihar Kordofan ta Arewa a safiyar Asabar, kamar yadda watsa labarai na cikin gida suka ruwaito.

Shafin Sudan News, ya ruwaito majiyoyin soji inda suke cewa sojojin sun kakkaɓo jirgi maras matuƙin samfarin ƙasar China a lokacin da yake wucewa ta saman birnin. An ce jirgin ya yi ƙoƙarin kai hari kan wuraren soja da na farar-hula a yammacin El-Obeid.

‘Yan gwagwarmaya sun yaɗa bidiyo a kafafen sada zumunta a lokacin da aka harbo jirgin, inda bayan an harbo shi jama’a suka yi ta ihu suna murna.

Babu wani bayani a halin yanzu game da jikkata ko wata ɓarnar daga harin da aka yi yunƙurin kaiwa.

Zugar jirage marasa matuƙa

RSF ta kai harin jiragen sama marasa matuki a ranar Juma'a, inda ta kai harin a wasu wurare a birnin Omdurman na Jihar Khartoum da kuma Atbara a Jihar River Nile, in ji wannan majiya.

A ranar Alhamis, sojojin Sudan sun ce makaman kariyarsu ta sama sun daƙile zugar jiragen sama marasa matuƙa da suka nufi Omdurman da ke yammacin Khartoum, da kuma garin Atbara a arewacin ƙasar.

Hukumomin Sudan sun zargi RSF da ƙara kai hare-hare ba iyaka da jiragen sama marasa matuƙa a kan farar-hula a Khartoum da sauran birane, ko da yake kungiyar ba ta mayar da martani a bainar jama'a kan tuhumar ba.

Tun daga 15 ga Afrilun 2023, sojojin Sudan da RSF suke yaƙi da juna inda har zuwa yanzu an kasa yin sulhu.

Wannan rikici na Sudan ya yi sanadiyyar mutuwar dubban mutane da kuma tilasta wa miliyoyin mutane guduwa daga gidajensu.

Rumbun Labarai
Sabbin hotunan tauraron dan'adam sun gano alamun 'kaburburan bai-daya a El-Fasher a Sudan
MDD ta yi gargaɗin cewa yaƙin Sudan na gurgunta tattalin arzikin Sudan ta Kudu
Trump ya ce bai kamata Afirka ta Kudu ta kasance cikin G20 ba, ba zai je taronta a Johannesburg ba
'Yan Sudan sun ba da mummunan labarin yi wa mata fyade yayin da suke tserewa daga Al Fasher
An kashe mutane 40 a harin da aka kai wa taron jana'iza a yankin Kordofan na Sudan: MDD
Yadda biranen Afirka mafiya tsafta suke bayyana sauyin da ake samu a nahiyar
Sojojin Ruwa na Ghana sun kama ‘yan Nijeriya 10 da suka ɓuya a jirgin ruwan Panama a Tema
Harin jirgin sama maras matuƙi na RSF ya kashe mutane da dama a lardin Kordofan na Arewa a Sudan
Fiye da mutum 1,500 sun rasa matsugunansu a Sudan sakamakon taɓarɓarewar tsaro: MDD
Dakarun RSF sun kashe mata 300, sun yi wa 25 fyaɗe cikin awa 48 a Al Fasher – Minista
Amurka ta buƙaci a tattauna domin kawo ƙarshen yaƙin Sudan, ba amfani da ƙarfin soja ba
Ana fargabar dubban mutane na cikin 'mummunan hatsari' a birnin Al Fasher na Sudan da RSF ta ƙwace
Shugabar Tanzania Samia Hassan ta lashe zaɓen ƙasar da kashi 97.66 cikin 100
Tchiroma Bakary: Sojojin Kamaru sun yi wa jagoran 'yan adawar kasar rakiya zuwa wuri mai 'aminci'
Kudirin 1325 ya cika shekara 25: Me ya sa dole Afirka ta jagoranci samar da zaman lafiya a duniya
Dubban mutane sun tsere daga North Kordofan yayin da RSF ta zafafa kai hari a yankin Darfur na Sudan
Fararen-hula 177,000 sun maƙale a Al Fasher na Sudan, yayin da RSF ke ci gaba da kisa - Likitoci
Rundunar RSF ta amsa aikata 'take haƙƙi' a Al Fasher na Sudan
Kenya ta tabbatar da mutuwar mutum 11 'yan yawon bude ido a hatsarin jirgin da aka yi a kasar
Nijar da Chadi za su ƙaddamar da aikin yi wa dabbobi rigakafi a Diffa