| Hausa
DUNIYA
2 minti karatu
Sojojin Isra'ila suna ci gaba da rusa gidaje da harba makaman atilare Gaza, duk da tsagaita wuta
Rahotannin na zuwa ne a daidai lokacin da Ma'aikatar Lafiya ta Gaza da MDD suka yi gargaɗin cewa ana ci gaba da kisa duk da yarjejeniyar tsagaita wuta ta 10 ga Oktoba, inda aka kashe Falasɗinawa fiye da 340 aka kuma jikkata kusan 900.
Sojojin Isra'ila suna ci gaba da rusa gidaje da harba makaman atilare Gaza, duk da tsagaita wuta
Motocin sojojin Isra'ila suna ajiye kusa da gine-gine rugujajju bayan hare-haren sojojin Isra'ila a unguwar Shijaiya ta birnin Gaza, Nuwamba 5, 2025.
25 Nuwamba 2025

Sojojin Isra'ila sun rusa gidaje da harba makaman atilare a yankuna da ke ƙarƙashin ikonsu a Gaza, suna ƙara saɓa wa yarjejeniyar tsagaita wuta.

Shaidu sun faɗa wa kamfanin dillancin labarai na Anadolu cewa sojojin sun rushe wasu gidaje a unguwar Shujaiya ta birnin Gaza, a arewacin yankin, wanda yake cikin yankin da rundunar ke iko da shi.

A kudu, shaidu sun ce an harba makaman atilare na Isra'ila sassan gabas a Khan Younis waɗanda ba a ƙarƙashin ikon Isra’ila suke ba.

Babu ƙarin bayani kan irin ta’adin da aka yi.

A cewar Hukumar Kariya ta Fararen Hula ta Gaza, an kashe Falasɗinawa biyu kuma wasu da dama sun ji rauni a harin da aka kai wani gida a unguwar Al-Nasr ta birnin Gaza da yammacin Litinin, lokacin da wani bam na Isra'ila ya fashe.

Riyad Mansour, Jakadan Falasdinu a Majalisar Dinkin Duniya, ya shaida wa Kwamitin Tsaro a ranar Litinin cewa tun bayan fara tsagaita wuta a ranar 10 ga Oktoba, sojojin Isra'ila suna kashe yara Falasɗinawa biyu a kowace rana a Gaza, yayin da adadin waɗanda suka jikkata da kuma suka mutu ya kai 1,000, a cewarsa.

A cewar Ma'aikatar Lafiya ta Gaza, aƙalla Falasɗinawa 342 ne aka kashe, kuma kusan 900 sun ji rauni sakamakon hare-haren sojojin Isra'ila, tun lokacin da tsagaita wuta ya fara.

Tun daga Oktoba 2023, sojojin Isra'ila sun kashe kusan mutane 70,000 a Gaza, mafi yawansu mata da yara, kuma sun jikkata fiye da mutane 170,900 a lokacin yakin shekaru biyu na kisan ƙare dangi, wanda ya rusa mafi yawancin yankin.