| hausa
NIJERIYA
3 minti karatu
Tinubu ya yi ganawar sirri da manyan jami'an tsaron Nijeriya
Da yake bayani ga manema labarai bayan ganawar, babban hafsan sojin ƙasan Nijeriya Waidi Shaibu ya ce sun samu labari mai kyau daga jihar ƙwara inda mutane 38 da aka yi garkuwa da su daga cocin suka koma ga iyalansu.
Tinubu ya yi ganawar sirri da manyan jami'an tsaron Nijeriya
Shugaba Tinubu ya yi wannan ganawar ne a ranar Lahadi da dare
3 awanni baya

Shugaba Tinubu ya yi ganawar sirri da manyan hafsoshin tsaro na Nijeriya a fadar gwamnatin ƙasar da ke Abuja.

Ganawar da suka yi ranar Lahadi ta samu halartar babban hafsan tsaron Nijeriya, Janar Olufemi Oluyode da babban hafsan sojin saman Nijeriya, Air Vice Marshal Kelvin Aneke da babban hafsan sojin ruwan Nijeriya, Rear Admiral Idi Abbas da kuma babban hafsan tattara bayanan sirrin sojin Nijeriya, Manjo Janar EAP Undiendeye ba babban hafsan sojin ƙasan Nijeriya, Manjo Janar Waidi Shaibu.

Kazlika waɗanda suka halarci zaman sun haɗa da Sufeto Janar na ‘yan sandan Nijeriya, Kayode Egbetokun, da babban darakatan hukumar tsaro ta farin kaya (DSS), Tosin Ajayi.

Da yake bayani ga manema labarai bayan ganawar, babban hafsan sojin ƙasan Nijeriya Waidi Shaibu ya ce sun samu labari mai kyau daga jihar ƙwara inda mutane 38 da aka yi garkuwa da su daga cocin suka koma ga iyalansu.

“Kuma an samu ci gaba a jihar Neja inda kimanin mutum 51 daga cikin ɗaliban suka koma ga ‘yan wansu. A jihar Kebbi, matakanmu na samun sakamako mai kyau. Ana samun ci gaba sosai a wannan fannin,” a cewar Janar Shaibu.

 “Kuma dukkannin jam’ian tsaro suna wurin inda suka zagaye dukkan wurin. Inda muke tsammanin za mu samu labari daga wannan wurin,” in ji shi.

Shi ma shugaban Nijeriyar, Bola Ahmed Tinubu, ya ce ganawar ta yi nazari kan rahotanni na baya bayan nan da kuma ɗaukar ƙwararan matakai domin tabbatar da zaman lafiya a yankunan.

Ina ci gaba da samun bayanai kuma na ba da umarni ga hukumomin tsaronmu su ɗauki mataki cikin sauri da seti da kuma jajircewa,” in ji shugaban ƙasar a wani saƙon da ya wallafa a shafinsa na Facebook.

A matsayina na shugaban ƙasa, na jajirce sosai a kan tsaron ‘yan Nijeriya. Waɗanda suke barazana ga zaman lafiya da tsaron ƙasarmu, za su fuskanci cikakkiyar uƙubar doka,” a cewar shugaban ƙasar.

Cikin ‘yan ƙwanakin nan dai Nijeriya ta fuskanci hare-haren ‘yan ta’adda da suka sace mutane a jihohin Kwara da Kebbi da Neja.

A jihar Kwara dai, ‘yan bindiga sun sace mutane a lokacin da suke ibada a wani coci da ke garin Eruku.

A jihar Kebbi kuma ‘yan bindiga sun saci ɗalibai 25  ‘yan makarantar sakandare ta ‘yan mata ta GGCS da ke garin Maga. Biyu daga cikin ɗaliban sun kuɓuce daga hannun masu garkuwa da mutane.

Sai kuma jihar Neja inda ‘yan bindiga suka saci mutum 315 a makaranatar firamare ta ɗarikar Katololika inda daga baya 50 daga cikinsu suka kuɓuce kuma suka koma ga iyalansu.

 Sai dai shugaban ƙasar ya yi shelar cewa an ‘yanta mutum 38 da aka yi garkuwa da su a jihar Kwara kuma ya sha alwashin cewa zai yi abin da ya dace domin tabbatar da tsaron ‘yan Nijeriya.

 

Rumbun Labarai
Yadda ta kaya a zaman 'yan majalisar Amurka kan zargin yi wa Kirisotci kisan kiyashi a Nijeriya
‘Yan bindiga sun sace ɗalibai da ma’aikata a wata makaranta a Jihar Neja
Jagoran ƴan-awaren Biafra: Babbar Kotu a Nijeriya ta yanke wa Nnamdi Kanu hukuncin ɗaurin rai da rai
'Yan Nijeriya miliyan 45 suna bahaya har yanzu a waje — Ministan Muhalli
Ribadu ya jagoranci wata tawagar Nijeriya mai ƙarfi zuwa Amurka kan zargin kashe Kiristoci a ƙasar
Kotu ta yanke wa wani shugaban ISWAP da ya tsara hare-haren kano na 2012 ɗaurin shekara 20
Tinubu ya ɗaga tafiyarsa tarukan G20 da AU-EU saboda yanayin rashin tsaro da ake ciki a Nijeriya
Majalisar Dattawan Nijeriya ta nemi a ɗauki ƙarin sojoji 100,000 don magance rashin tsaro
Tinubu ya yi alhinin mutuwar Janar Uba da 'yan ta'adda suka kashe a Borno
Majalisar Dokokin Amurka za ta binciki zargin yi wa Kiristoci kisan kiyashi a Nijeriya ranar Alhamis
Gwamnatin Jihar Katsina za ta shirya muƙabala tsakanin Yahya Masussuka da sauran Malaman Musulunci
Babban hafsan sojin Nijeriya ya je Jihar Kebbi ya nemi  a tsaurara neman 'yan matan da aka sace
Gwamnatin Nijeriya ta umarci jami’an tsaro su kuɓutar da ɗalibai mata da aka sace a Jihar Kebbi
Nijeriya tana tattaunawa kan tsaro da Amurka bayan barazanar Trump: Yusuf Tuggar
Gwamnatin Nijeriya ta ƙaddamar da tallafin jarin N50m ga ɗalibai a fannin ƙirƙire-ƙirƙire
Rikicin PDP: Ɓangaren Wike ya yi watsi da kora yayin da jihohi huɗu ke ƙalubalantar Makinde
‘Yan sandan Nijeriya sun tabbatar da sace ɗalibai ‘yan mata 25 a Kebbi
Sojojin Nijeriya sun daƙile kwanton-ɓauna, sun yi watsi da jita-jitar sace wani janar na soja
Kasafin kuɗin gwamnatin kano na 2026 zai haura naira tiriliyan ɗaya - Gwamna Abba Kabir
Yaya karawar Nijeriya da Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo za ta kasance?