| hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
Ɗalibai 50 cikin fiye da 300 da aka sace daga makarantar St. Mary a Jihar Neja sun tsere - CAN
A cikin wata sabuwar sanarwa da ƙungiyar ta CAN ta fitar a ranar Lahadi, ɗalibai 50 ɗin da suka sun riga sun haɗu da iyalansu.
Ɗalibai 50 cikin fiye da 300 da aka sace daga makarantar St. Mary a Jihar Neja sun tsere - CAN
Dalibai 50 ne suka tsere daga cikin kimanin 300 a cewar CAN
21 awanni baya

Ɗalibai hamsin da aka sace daga Makarantar Sakandare da Firamare ta St. Mary’s da ke Papiri, a Karamar Hukumar Agwara ta Jihar Neja, sun tsere daga hannun masu garkuwa da su.

’Yan bindiga sun kai hari a makarantar cikin daren Juma’a, inda suka harbi mai gadi sannan suka yi awon gaba da fiye da dalibai 200, tare da malamai 13 da ma’aikatan da ba na koyarwa ba.

A cikin rahotonsa na farko game da lamarin, Shugaban Kungiyar Kiristoci ta Nijeriya (CAN) a Jihar Neja, Most Rev. Bulus Dauwa Yohanna, wanda shi ma mai makarantar ne, ya ce an sace ɗalibai 215 tare da ma’aikata 12.

Amma zuwa ranar Asabar, ya ce dalibai 88 ba a san inda suke ba.

Sai dai a cikin wata sanarwa da mai taimaka masa, Daniel Atori, ya fitar a madadinsa a ranar Lahadi, Faston ya bayyana cewa ɗaliban da suka tsere a ranar Asabar sun riga sun haɗu da iyalansu.

 “Wannan sanarwa ce ga jama’a cewa a ranar Lahadi, 23 ga Nuwamban 2025, mun samu labari mai daɗi cewa dalibai hamsin sun tsere kuma sun koma wurin iyayensu,” in ji sanarwar.

Rev. Yohanna ya ce makarantar tana gudanar da tsarin kwana da na jeka-ka-dawo.

A cewarsa, sashen firamare na da ɗalibai 430, inda 377 ke kwana a makaranta, 53 kuma masu ‘yan jeka-ka-dawo.

Yayin bayani kan waɗanda har yanzu ba a san halin da suke ciki ba, ya bayyana:
“Yanzu haka, baya ga ɗalibai 50 da suka tsere suka kuma koma gida, muna da dalibai 141 da ba a sace su ba. A halin da muke ciki yanzu, ɗalibai 236, da yara uku na ma’aikata da ɗalibai 14 na sakandare da ma’aikata 12 suna nan a hannun masu garkuwa da su.”

 

 

Rumbun Labarai
Yadda ta kaya a zaman 'yan majalisar Amurka kan zargin yi wa Kirisotci kisan kiyashi a Nijeriya
‘Yan bindiga sun sace ɗalibai da ma’aikata a wata makaranta a Jihar Neja
Jagoran ƴan-awaren Biafra: Babbar Kotu a Nijeriya ta yanke wa Nnamdi Kanu hukuncin ɗaurin rai da rai
'Yan Nijeriya miliyan 45 suna bahaya har yanzu a waje — Ministan Muhalli
Ribadu ya jagoranci wata tawagar Nijeriya mai ƙarfi zuwa Amurka kan zargin kashe Kiristoci a ƙasar
Kotu ta yanke wa wani shugaban ISWAP da ya tsara hare-haren kano na 2012 ɗaurin shekara 20
Tinubu ya ɗaga tafiyarsa tarukan G20 da AU-EU saboda yanayin rashin tsaro da ake ciki a Nijeriya
Majalisar Dattawan Nijeriya ta nemi a ɗauki ƙarin sojoji 100,000 don magance rashin tsaro
Tinubu ya yi alhinin mutuwar Janar Uba da 'yan ta'adda suka kashe a Borno
Majalisar Dokokin Amurka za ta binciki zargin yi wa Kiristoci kisan kiyashi a Nijeriya ranar Alhamis
Gwamnatin Jihar Katsina za ta shirya muƙabala tsakanin Yahya Masussuka da sauran Malaman Musulunci
Babban hafsan sojin Nijeriya ya je Jihar Kebbi ya nemi  a tsaurara neman 'yan matan da aka sace
Gwamnatin Nijeriya ta umarci jami’an tsaro su kuɓutar da ɗalibai mata da aka sace a Jihar Kebbi
Nijeriya tana tattaunawa kan tsaro da Amurka bayan barazanar Trump: Yusuf Tuggar
Gwamnatin Nijeriya ta ƙaddamar da tallafin jarin N50m ga ɗalibai a fannin ƙirƙire-ƙirƙire
Rikicin PDP: Ɓangaren Wike ya yi watsi da kora yayin da jihohi huɗu ke ƙalubalantar Makinde
‘Yan sandan Nijeriya sun tabbatar da sace ɗalibai ‘yan mata 25 a Kebbi
Sojojin Nijeriya sun daƙile kwanton-ɓauna, sun yi watsi da jita-jitar sace wani janar na soja
Kasafin kuɗin gwamnatin kano na 2026 zai haura naira tiriliyan ɗaya - Gwamna Abba Kabir
Yaya karawar Nijeriya da Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo za ta kasance?