| hausa
AFIRKA
2 minti karatu
AfDB zai ba Nijar CFA biliyan 98.7 domin magance matsalar ruwa ta shekara 70 a Zinder
Firaministan Nijar Ali Mahaman Zeine ya bayyana girman matsalar ruwa a wannan yankin wadda ya ce matsala ce tun ta zamanin mulkin mallaka, ya kuma ce ko tashar samar da ruwa ta farko ta Aroungouza wadda aka gina a 1955 ba ta taɓa magance matsalar ba.
AfDB zai ba Nijar CFA biliyan 98.7 domin magance matsalar ruwa ta shekara 70 a Zinder
AfDB ya amince domin bayar da kimanin CFA biliyan 98.7 domin sake gina hanyoyin samun ruwan sha da tsaftar muhalli.
15 Nuwamba 2025

Bayan shafe shekaru 70 ana fama da ƙarancin ruwa da kuma samar da mafita maras ɗorewa lokaci bayan lokaci, da alamu yankin Zinder da kewaye ya samu mafita ta dindindin

Bankin Ci gaban Tattalin Arzikin Afirka AfDB ya amince domin bayar da kimanin CFA biliyan 98.7 domin sake gina hanyoyin samun ruwan sha da tsaftar muhalli.

Waɗannan maƙudan kuɗaɗen ba Zinder kaɗai za ta amfana da su ba, har da Mirriah da wasu ƙauyuka 14 da ke maƙwabtaka, wanda yawan jama’arsu ya kai mutum 700,000 inda fiye da rabinsu mata ne.

Ga waɗannan al’ummomin da suka daɗe suna wahala, ruwa — wanda ya kasance yana musu matuƙar wahalar samu kuma mai matuƙar muhimmanci — a ƙarshe zai iya zama abin da za su iya samu cikin sauƙi sannan kuma ya kasance wani jigo na samun ci gaba, tare da kawo ƙarshen matsalar ruwan da ta yi tasiri matuƙa a ɓangaren lafiya da tattalin arziki da rayuwar yau da kullum ta jama’a tsawon shekaru.

A jawabin da ya gabatar, Firaiministan Nijar Ali Mahaman Lamine Zeine bai yi ƙoƙarin rage girman matsalar ba. Ya bayyana ta a matsayin wata “matsala da ta addabi yankin tun zamanin mulkin mallaka,” wadda ma tashar farko ta shan ruwa ta Aroungouza, wadda aka gina a 1955, ba ta taɓa magance ta gaba ɗaya ba.

Zinder, birni na biyu mafi girma a ƙasar, ya shafe shekaru yana fama da wannan matsala, yayin da jama’a ke ƙaruwa, albarkatu suna raguwa, kuma illolin sauyin yanayi na ƙara bayyana.

“Babban burin wannan aikin shi ne inganta rayuwar jama’ar Zinder cikin ɗorewa,” in ji shi. “Zai magance buƙata ta haƙiƙa, buƙata mai muhimmanci ga mutanen wannan birni da na yankunan da ke kewaye, waɗanda tsawon shekaru suke fama da ƙarancin ruwa,” in ji Zeine.

 

Rumbun Labarai
Ghana za ta tura injiniyoyin soji don taimakawa wajen sake gina Jamaica bayan afkuwar guguwa
Mutane 70 sun ɓace bayan jirgin ruwa ɗauke da mutum 120 ya kife a DRC
Wata ƙungiya ta zargi kamfanin Nestle da sayar wa Afirka abincin jarirai mai sikari da yawa
Ranar Makewayi ta Duniya: Kundin tsafta na Afirka don inganta lafiya da mutunci
Sabon Alƙalin Alƙalan Ghana Baffoe-Bonnie ya fara aiki
An raba fiye da mutum 100,000 da gidajensu a Al Fasher na Sudan daga lokacin da RSF ta ƙwace birnin
Kafafen watsa labaran Afirka: Abokan kawo ci gaba da ake mantawa da su
Za a ƙara farashin man fetur a Ghana
Ruftawar mahaƙar ma’adanai ta yi ajalin aƙalla mutum 32 a DRC
An samu rahotanni 32 na yi wa 'yan mata fyade bayan RSF ta ƙwace birnin Al Fasher - Likitoci
Mutum huɗu sun rasu bayan jiragen ruwa biyu na 'yan ci-rani sun kife a gaɓar tekun Libya
DR Congo da M23 sun cim ma yarjejeniyar zaman lafiya 'ta tarihi' a Qatar
MDD ta yi gargaɗi kan ƙazancewar yaƙin Sudan, ta yi kira kan barin shigar da kayan agaji
An gabatar da GH¢302bn a matsayin kasafin kuɗin Ghana na 2026 ga majalisar dokokin ƙasar
Sojojin Sudan sun daƙile harin RSF kan filin jirgin sama da dam a arewacin ƙasar
Rubio ya nemi a daina bai wa RSF makamai, ya ɗora wa rundunar laifi kan kashe-kashe a Al Fasher
Dalilin da ya sa TikTok ya goge bidiyoyi miliyan 1.5 da 'yan Uganda suka wallafa
Mutum 12 sun mutu a turmutsutsun neman aikin soja a Ghana – Rahotanni
Mahaucin Al Fasher: Yadda hotonsa ya zama alamar bakin cikin Sudan
UN Women: Mata da 'yan mata 11M suna fama da matsanancin ƙarancin abinci a Sudan sakamakon yaƙi