| Hausa
NIJERIYA
3 minti karatu
Naira da hannayen-jari Nijeriya sun faɗi sakamakon barazanar da Trump ya yi ta kai hari ƙasar
Kazalika darajar Naira ta faɗi a kasuwar bayan fage zuwa N1,455 kan kowace dalar Amurka, lamarin da ya nuna ƙarin fargabar masu zuba jari da kuma matsin neman kuɗaɗen waje.
Naira da hannayen-jari Nijeriya sun faɗi sakamakon barazanar da Trump ya yi ta kai hari ƙasar
Darajar kuɗin Nijeriya dai ta yi ƙarfi kafin kalaman na Trump / Reuters

Kasuwannin kuɗaɗe da hannayen-jari na Nijeriya sun fara watan Nuwamban shekarar 2025 da ƙafar hagu  inda ƙimar kuɗin ƙasar Naira da hannayen-jari suka faɗi  bayan shugaban Amurka, Donald Trump ya yi barazanar yiwuwar kai harin soji Nijeriya kan zargin yi wa Kiristoci kisan gilla.

Alƙaluma daga Babban Bankin Nijeriya sun nuna cewa naira, wadda aka sayar 1,421 ga kowace dalar Amurka ta koma 1,436 ga dalar Amurka ranar Litinin inda darajarta ta faɗi da kashi 1.03 cikin 100 ko kuma da naira 14.61 a yini ɗaya, kamar yadda jaridar Punch ta Nijeriya ta ruwaito.

Kazalika darajar kuɗin ta faɗi a kasuwar bayan fage zuwa N1,455 ga dalar Amurka, lamarin da ya nuna ƙarin fargabar masu zuba jari da kuma matsin neman kuɗaɗen waje.

Masu AlakaTRT Afrika - Donald Trump ya ayyana Nijeriya a matsayin ƙasar da ake yi wa Kiristoci kisan gilla

Faɗuwar ƙimar kuɗin ta biyo bayan zargin da Trump ya yi a wani saƙo a shafinsa na sada zumunta na Truth Social cewa aka yi wa Kiristoci kisan gilla a ƙasar, inda ya ayyana Nijeriya matsayin wata ƙasa wadda ke buƙatar sa ido na musamman.

Kazalika ya umarci Ma’aikatar Yaƙin Amurka ta shirya domin yiwuwar kai hari “domin kawar da 'yan ta'adda masu kaifin kishin Musulinci waɗanda ke yin wannan ta’asa.”

Nan-take kalamansa suka soma tasiri a kasuwannin hannayen-jari. A kasuwar hannayen-jarin Nijeriya darajar kasuwar ta ragu da kashi 0.25 cikin 100 inda kasuwar ta ƙarƙare da maki 153,739.11 a ranar Litinin, lamarin da ya rage ribar shekara zuwa shekara zuwa kashi 49.37 cikin 100. Ƙimar kasuwar kuma ta ragu da naira biliyan 245.88, inda ƙimar ta tsaya a naira tiriliyan 97.58t.

Faɗuwar ta fi yawa ne daga yadda aka sayar da hanayen-jarin Aradel Holdings (kashi -9.21 cikin 100) da kuma Access Corporation (kashi -3.07 cikin 100). Ƙarfin gwiwar masu jari dai ya yi rauni inda farashin hannayen-jarinkamfanoni 38 inda farashin hannayen-jarin kamfanoni 19 suka faɗi.

Hannun-jarin kamfanin Union Dicon ne ya fi samun riba (kashi +9.93 cikin 100), yayin da farashin hannayen-jarin kamfanin Honeywell Flour Mills yake kan gaba a cikin waɗanda suka faɗi (kashi -10.00 cikin 100).

Kazalika hada-hadar hannayen-jari ta ragu sosai inda adadi da ƙimar hannayen-jarin da aka saya ko sayar suka faɗi da kashi 87.94 cikin 100 da kuma kashi 44.64 cikin 100, zuwa hannayen-jari miliyan 627.5 masu kimar naira biliyan N25bn. Bankin United Bank for Africa (UBA) ya fi mamaye harkar, inda aka yi musayar hannayen-jarinsa miliyan  136.8 (kashi 21.8 cikin 100 na adadin hannayen-jarin) wanda kimarsu ta kai naira biliyan N5.5bn (kashi 22.2 cikin 100 na adadin ƙimar kasuwar).

Rumbun Labarai
Za mu tabbatar Tinubu ya lashe zaɓen Nijeriya na 2027— Abdulaziz Yari
Tinubu ya buƙaci jami'an yaƙin neman zaɓensa su bayyana wa ‘yan Nijeriya nasarorin gwamnatinsa
Tinubu ya yi umarnin kama wani mutum, ya dakatar da manyan sakatarori bayan gano wata hukuma ta bogi
EFCC ta janye ƙarar da ta shigar da Maryam Shehu da Abubakar Shuraim kan zargin ɓata suna
Iyalai sun yi zanga-zanga a Nijeriya kan yaran da aka sace kusan kwanaki 100 da suka gabata
Kira a mayar da tallafin fetur jahilci ne kan yadda ake tafiyar da tattalin arziki - Tinubu
Hatsarin kwale-kwale ya yi ajalin mutum aƙalla 50 a Jihar Sokoto ta Nijeriya
Atiku ya sha alwashin mayar da tallafin man fetur idan aka zaɓe shi shugaban Nijeriya a 2027
Sufeto Janar na ‘Yansandan Nijeriya ya yi gargaɗi kan ɗora wa mutane laifuka bisa ƙabila ko addini
An buɗe yaƙin neman zaɓen shugaban Nijeriya na 2027 a hukumance
Tsohon Shugaban Nijeriya Jonathan ya yi gargaɗi kan yadda gwamnoni ke tarewa a jihohin da ake zaɓe
Ana zargin Lakurawa da kashe aƙalla mutum 28 a masallaci a Sokoto
Akwai ramukan haƙar ma'adinai fiye da 4,000 da aka yi watsi da su a Filato — Alake
Manoma biyar sun rasu bayan kwale-kwale ya kife a Jihar Neja ta Nijeriya
‘Yansandan Nijeriya sun kama wani mutum kan zargin watsa wa matarsa fetur da cinna mata wuta
Sake cin zaɓen gwamnan Osun tabbaci ne cewa dimokuraɗiyya za ta ci gaba da bunƙasa a Nijeriya—Tinubu
INEC ta ayyana Ademola Adeleke a matsayin wanda ya lashe zaɓen gwamnan jihar Osun
Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya yi kira ga 'yan Nijeriya da ke ketare su zuba jari a Nijeriya
Tinubu ya yi alƙawarin farfaɗo da matatun man Nijeriya da suka jima ba sa aiki yadda ya kamata
Shugabannin addinai a Nijeriya sun sa hannu kan yarjejeniyar inganta zaman lafiya da fahimtar juna