Dalilin da ya sa TikTok ya goge bidiyoyi miliyan 1.5 da 'yan Uganda suka wallafa
TikTok ta goge bidiyoyi miliyan 1.5 da 'yan Uganda suka wallafa
Dalilin da ya sa TikTok ya goge bidiyoyi miliyan 1.5 da 'yan Uganda suka wallafa
TikTok ya goge bidiyoyi miliyan 189 tsakanin watan Afrilu zuwa Yunin 2025 a faɗin duniya saboda karya ka'idojin al'umma da manhajar ta gindaya.
kwana ɗaya baya

Manhajar Tiktok ta goge bidiyoyi fiye da miliyan 1.5 waɗanda ‘yan Uganda suka wallafa saboda abin da ta kira ‘‘keta dokokin manhajar.’’

A cewar wata jarida a ƙasar da ke yankin gabashin Afirka, an goge bidiyoyin ne daga Tiktok tsakanin watan Afrilu zuwa Yunin 2025, manhajar ta bayyana cewa suna ɗauke da kalaman kiyayya, da na ƙarya da kuma ba batsa.

Bayan wannan mataki na kwanan nan da aka ɗauka, Uganda ta zama ƙasa ta 29 a cikin jerin ƙasashen duniya da aka fi goge bidiyoyi a TikTok cikin watanni uku.

Bidiyoyi ‘yan Uganda miliyan 1.5 da aka goge ya zarce yawan na ‘yan Kenya 592,000 da aka goge, kasar da ke daya daga cikin ƙasashen duniya da ke amfani da Tiktok a duniya.

Matakin ya shafi dubban mutane

An sauƙe aƙalla bidiyoyi 420,000 na ‘yan Afirka ta Kudu, yayin da aka goge fiye da bidiyoyi 310,000 na ‘yan Nijeriya.

A duniya baki ɗaya, TikTok ya goge bidiyoyi miliyan 189 saboda karya ka'idojin al'umma na manhajar tsakanin watan Afrilu zuwa Yunin 2025.

Manhajar TikTok ita ce hanyar sadarwa ta biyu mafi yawan amfani idan aka kwantanta da sauran shafukan sada zumunta a Uganda, baya ga WhatsApp da ake aika saƙonnin cikin sauri.

Masu AlakaTRT Afrika - Masu fafutuka suna son a sauya tsarin TikTok saboda gazawar shafin daga kare yara

Hukumar Sadarwa ta Uganda (UCC) ta bayyana cewa ƙasar ta yankin Gabashin Afirka tana da masu amfani da manhajar TikTok mutum miliyan 8.8, wanda ya kai kusan kashi 17% na yawan jama'ar kasar baki daya.

A cewar TikTok, matakin da aka ɗauka na goge bidiyoyin ‘yan TikTok ya shafi waɗanda suka nuna barasa, kwayoyi, da makamai, da kuma yada tsiraici.

A lokuta da dama, bidiyoyin ‘yan Uganda sun sha jan hankali inda aka yi kama mutane a lokuta daban-daban, inda ake zarginsu da amfani da manhajar don cin mutuncin Shugaba Yoweri Museveni da iyalansa.

An yanke wa daya daga cikin wadanda aka zargi, Edward Awebwa, hukuncin daurin shekaru shida a gidan yari a watan Yulin 2024, yayin da wani, Emmanuel Nabugodi, aka yanke masa hukuncin zaman gidan yari na tsawon watanni 32 a watan Nuwamban shekarar saboda amfani da TikTok da yi wajen cin mutuncin iyalan shugaban ƙasar.

Rumbun Labarai
UN Women: Mata da 'yan mata 11M suna fama da matsanancin ƙarancin abinci a Sudan sakamakon yaƙi
WHO ta bayyana damuwa kan karuwar masu ciwon siga a Afirka
Kisan kare dangi a boye da bayyane: Gushewar jinkai a Al Fasher
An ba da belin dan Gaddafi bayan da ya shafe shekaru 10 a tsare a Lebanon
Gwamnatin Trump 'ta aika wa Equatorial Guinea dala miliyan 7.5' don ta karɓi waɗanda Amurka ta kora
Ƙasashe fiye da 20 sun yi Allah wadai da RSF kan kashe-kashen da take yi a Sudan
Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya ya yi kira da a dakatar da zubar da jini a Sudan
Paul Biya na Kamaru: Dan siyasar da zai ci gaba da yin mulki har sai ya kai shekara 99?
Hare-haren RSF sun kori ƙarin dubban mutane daga Darfur da Kordofan na Sudan
RSF ta binne gawawwaki a kabarin bai-ɗaya, ta ƙone wasu domin 'ɓoye laifukan yaƙi': Likitocin Sudan
Sojojin Sudan sun harbo jirgi maras matuƙi na RSF a Kordofan ta Arewa
Dakarun Nijar sun cafke muggan makamai da aka yi safararsu daga Libya, sun kama masu safarar ƙwayoyi
RSF ta Sudan ta kai hare-hare a Jihar Khartoum da birnin Atbara bayan amincewa da tsagaita wuta
Paul Biya na Kamaru: Shugaban da ya fi tsufa a duniya ya sha rantsuwar kama aiki karo na takwas
Hatsarin mota ya yi ajalin fiye da mutum 1,000 a Nijar a shekarar 2023, fiye da 12,000 sun jikkata
Sabbin hotunan tauraron dan'adam sun gano alamun 'kaburburan bai-daya a El-Fasher a Sudan
MDD ta yi gargaɗin cewa yaƙin Sudan na gurgunta tattalin arzikin Sudan ta Kudu
Trump ya ce bai kamata Afirka ta Kudu ta kasance cikin G20 ba, ba zai je taronta a Johannesburg ba
'Yan Sudan sun ba da mummunan labarin yi wa mata fyade yayin da suke tserewa daga Al Fasher
An kashe mutane 40 a harin da aka kai wa taron jana'iza a yankin Kordofan na Sudan: MDD