Gwamnatin Nijeriya ta ce 'an warware taƙaddamar diflomasiyyar’ da ta faru kwanan baya tsakaninta da Amurka, inda Shugaba Donald Trump ya yi barazanar shigar da sojoji kan zargin yi wa Kiristoci kisan gilla.
Trump ya soki ƙasar yammacin Afirkan a watan Oktoba da Nuwamba, yana cewa Kiristoci a can suna fuskantar 'kisan gilla’ a yanayi na mawuyacin halin rashin tsaron Nijeriya.
“Rikicin diflomasiyya da ya faru kwanan baya da Amurka an warware shi kusan gaba ɗaya ta hanyar mu'amala mai ƙarfi da girmamawa, wanda ya haifar da ƙarfafa haɗin gwiwa tsakanin Amurka da Nijeriya,” in ji Ministan Yaɗa Labaran Nijeriya Mohammed Idris a taron manema labarai na ƙarshen shekara a babban birnin tarayya, Abuja.
Gwamnatin Nijeriya da masana masu zaman kansu sun ƙi goyon bayan fassara matsalar rashin tsaron ƙasar a matsayin azabtarwa ta addini.
Yarjejeniyar agaji
Maganganun Idris sun biyo bayan karɓar tawagar wakilan majalisar dokoki ta Amurka da Nijeriya ta yi a farkon wannan wata.
A makon da ya gabata, Nijeriya ta kasance cikin kasashen da gwamnatin Trump ta sanya musu takunkumin biza da na shige-da-fice.
Nijeriya na fuskantar barazanar 'yanta'adda a arewa maso gabas, da kuma ƙungiyoyin 'yan fashi da makami waɗanda ke sata a ƙauyuka da sace mutane domin neman fansa a arewa maso yamma.
A lokacin da yake magana da 'yanjarida, Idris ya kare wata sabuwar yarjejeniyar agaji wadda za ta sa Washington ta bayar da dala biliyan 2.1, abin da Ma'aikatar Harkokin Waje ta Amurka ta bayyana a matsayin 'wanda zai fi mayar da hankali wajen inganta kiwaon lafiyar mabiya addinin Kiristanci.'
'Kowane ɗan Nijeriya zai kasance mai cin gajiyar wannan tsari,' in ji Idris.












