| Hausa
TURKIYYA
2 minti karatu
Dubban mutane sun yi gangami a Istanbul na goyon bayan Falasɗinawa
Gangamin wanda shugabannin addini da na ƙungiyoyin kare hakkin ɗan'adam suka jagoranta mai taken "Ba Za Mu Yi Shiru ba", wato “We Do Not Remain Silent” a Turancin Ingilishi, ya samu halartar ƙungiyoyi fiye da 400.
Dubban mutane sun yi gangami a Istanbul na goyon bayan Falasɗinawa
Participants waved banners reading “Justice for Palestine” and chanted against Israel’s actions. / TRT World
1 Janairu 2026

Dubban ɗaruruwan mutane ne suka yi gangami a birnin Istanbul domin nuna goyon baya ga Falasɗinawa, inda suka yi kira a kawo ƙarshen yaƙin kisan ƙare-dangin da Isra’ila take yi a Gaza.

Gangamin wanda shugabannin addini da na ƙungiyoyin kare hakkin ɗan'adam suka jagoranta mai taken "Ba Za Mu Yi Shiru ba", wato “We Do Not Remain Silent” a Turancin Ingilishi ya samu halartar ƙungiyoyi fiye da 400.

Mahalarta gangamin sun fito da asalatu ranar Alhamis inda suka soma da gudanar da sallar asubahi a manyan masallatan da suka haɗa da Ayasofya Grand Mosque, Sultanahmet, Fatih, Suleymaniye, da Eminonu Yeni Cami.

Daga nan, masu gangamin sun yi maci zuwa Gadar Galata, riƙe da tutocin Turkiyya da na Falasɗinu, kuma sanye da ƙyallayen Falasɗinawa waɗanda aka rubuta kamar “Daga Istanbul zuwa Gaza, dubban gaisuwa ga masu gwagwarmaya” da “A ‘Yanta Falasɗinu.”

Bilal Erdogan, shugaban Gidauniyar İlim Yayma, ya gabatar da jawabi ga mahalarta gangamin, inda ya jaddada goyon bayansu ga Falasɗinawa.

“Duk shekara, masu halartar irin gangami suna ƙara yawa, kuma a yau muna jin ƙarfi na ‘yan’uwantaka a matsayinmu na ‘yan ƙasa,” in ji shi, inda ya yi addu’o’i na samun ‘yanci ga mutanen da ke Falasɗinu da Birnin Ƙudus.

Sauran shugabannin ƙungiyoyin fararen-hula, waɗanda suka haɗa da Abdullah Ozdemir, shugaban AK Party reshen Istanbul, da shugaban ƙungiyar ONDER İmam Hatipliler Abdullah Ceylan, sun halarci macin.

Mahalarta gangamin sun riƙe kwalaye da aka rubuta “A Yi Adalci ga Falasɗinu” inda suka riƙa rera take na yin Allah wadai da Isra’ila.

Mutane sun riƙa raba shayi da biredin simit da miya a kan hanya ga masu gangamin.

‘Yansanda sun ƙarfafa matakan tsaro a kan hanya, ko da yake waɗanda suka shirya gangamin sun bayyana shi a matsayin wanda aka yi cikin lumana domin goyon bayan Falasɗinawa.

Mahalarta da dama sun bayyana fatan ganin shekarar 2026 ta kasance mai cike da adalci da zaman lafiya ga al’ummar Gaza da ke cikin uƙuba, inda suka bayyana gangamin a matsayin “babban saƙo na goyn baya” daga Istanbul ga duniya.

Rumbun Labarai
Filin jirgin saman Sabiha Gokcen na Istanbul ya karɓi fasinja fiye da miliyan 44 a cikin wata 11
Shugaban Turkiyya ya yi wa Firaiministan Libya ta'aziyya kan mutuwar babban hafsan sojin ƙasar
Turkiyya ta soki ta'addancin RSF a Sudan, ta yi kiran gaggawa don bayar da damar ayyukan jinƙai
Turkiyya ta kai rukunin farko na tantuna 30,000 da za ta kai Sudan a matsayin agaji
Turkiyya za ta ci gaba da fayyace gaskiyar abin da ke faruwa a Gaza: Erdogan
Shirin kawar da shara na Matar Shugaban Turkiyya ya tsara taswirar Ankara na karbar bakuncin COP31
Turkiyya ta kakkaɓo wani jirgi maras matuƙi da ya nufo sararin samaniyarta ta kan Bahar Aswad
Turkiya ta yi Allah wadai da harin da ya kashe sojojin wanzar da zaman lafiya 6 na MDD a Sudan
Turkiyya ta ba da sabbin shawarwari tsaro kan Bahar Aswad bayan ƙaruwar hari kan jiragen ruwa
Saƙon Turkiyya kan Gaza a taron MDD na watan Satumba ya bar Trump cikin tunani: Erdogan
Shugaba Erdogan ya yi gargaɗi kan mayar da Bahar Aswad fagen fama
Turkiyya tana bai wa zaman lafiya da tattaunawa mahimmanci - Shugaba Erdogan
An buɗe Taron Ilimi na Istanbul karo na biyar wanda Gidauniyar Maarif ta shirya
TRT ta fice daga taron EBU a yayin da mahalarta suka yi ce-ce-ku-ce kan shigar Isra'ila Eurovision
Yarjejeniyar zaman lafiya tsakanin Rasha da Ukraine za ta tsara makomar Turai: Fidan na Turkiyya
Turkiyya za ta karɓi baƙuncin manyan tarukan duniya a 2026: Shugaban Erdogan
Jirgin yaƙin Turkiyya maras matuƙi ya kafa tarihin harba wa wani jirgi makami a sararin samaniya
Fafaroma Leo na 14 ya ziyarci Masallacin Sultanahmet da ke Istanbul
An karrama Erdogan da Kambin WHO a Turai saboda ayyukan jinƙan Turkiyya a Falasdinu
A shirye Turkiyya take ta karɓi baƙuncin COP31, da taimakawa don sake gina Gaza: Erdogan