| Hausa
AFIRKA
2 minti karatu
Yaƙin Sudan: Sojojin Sudan sun ce sun yi wa sojojin RSF asara a Darfur da Kordofan
Sojin Sudan sun ce aikin da suka yi ta sama da ƙasa sun lalata ɗaruruwan motoci a cikin mako guda.
Yaƙin Sudan: Sojojin Sudan sun ce sun yi wa sojojin RSF asara a Darfur da Kordofan
Yakin Sudan ya barke a Afrilu 2023. HOTO / FAILE / Reuters
9 Janairu 2026

Sojojin Sudan sun ce sun yi wa Rundunar ‘Yan Sa-Kai ta (RSF) mummunar asara mai yawa yayin jerin harare-hare ta sama da ƙasa da aka gudanar a makon da ya gabata a yankunan Darfur da Kordofan.

A cikin wata sanarwa da ta fitar ranar Juma’a, rundunar ta ce dakarunta sun kai farmaki kan wuraren RSF, sun lalata kimanin motocin yaki 240 kuma sun kashe ɗaruruwan mayaƙa.

Sojojin sun ce harin ya kuma nufi abin da suka bayyana a matsayin wuraren kayan aikin sufuri da ayyukan RSF, ciki har da wuraren da suka shafi jiragen sama marasa matuki da wuraren ajiya, da kuma wurare a Filin Jirgin Sama na Nyala a Kudancin Darfur.

Sun ƙara da cewa dakarun ƙasa kuma sun samu nasarar korar mayaƙan RSF daga yankuna masu yawa a Darfur da Kordofan, kuma ana ci gaba da gudanar da ayyuka domin bin sauran 'yan kungiyar.

RSF ba ta yi martani ba kan bayanin sojojin har yanzu.

Fararen hula masu gudun hijira

A 'yan makonnin da suka gabata, rikici ya ƙaru a jihohin Kordofan uku na Sudan – Arewa, da Yamma da Kudu – inda fafatwar ɓangarorin biyu ta tilasta wa dubu-dubban fararen hula barin gidajensu.

Daga cikin jihohi 18 na Sudan, RSF ce ke iko da dukkan jihohi biyar na yankin Darfur a yamma, in ban da wasu sassan Arewacin Darfur da har yanzu rundunar soji ke iko da su. A gefe guda kuma, sojoji na riƙe da mafi yawan yankuna a cikin sauran jihohi 13 a kudu da arewa da gabas da tsakiyar ƙasar, ciki har da babban birnin ƙasar Khartoum.

Matsalar jin ƙai a Sudan ta ƙara ta'azzara tun bayan ɓarkewar yaƙi tsakanin sojoji da RSF a watan Afrilu 2023 kan saɓani na haɗe rundunar sojan ƙasar ta zama guda ɗaya, abin da ya yi sanadiyyar mutuwar dubu-dubatar mutane da kuma ƙaurar milyoyi.

Rumbun Labarai
Harin RSF na watan Oktoban 2025 a Al-Fasher na Sudan ya kashe aƙalla mutum 6,000: Rahoton MDD
AU: Shugabannin Afirka sun ƙaddamar da taron Ƙungiyar Tarayyar Afirka da batun ruwa da sauyin yanayi
Afirka ce kan-gaba wajen faɗaɗa samar da lantarki ta hasken rana a shekarar 2025: Rahoto
Gwamnatin Ghana ta ba da umarnin sarrafa kashi 50 cikin 100 na koko a cikin ƙasar
Sudan: Aƙalla mutum 21 sun mutu a hatsarin kwale-kwale a Kogin Nilu
Kasashe shida sun shiga Kwamitin Tsaro na Tarayyar Afirka
RSF ta kashe ƙananan yara a harin da ta kai wani masallaci a yankin Kordofan na Sudan
Saudiyya ta yi tur da RSF kan munanan ayyukanta a Al Fasher, ta buƙaci a ba da hanyar kai agaji
Mutum biyar sun mutu a hatsarin helikwaftan ɗaukar marasa lafiya a Libya
Yadda 'yan Somaliya suka gina wa tsohon shugaba ƙasarsu Farmaajo sabon gida
Sake dawo da ainihin martabar Afirka
RSF ta Sudan ta kai hari da jirgi maras matuƙi, ta kashe gomman mutane da yara
Dubban ‘yan kasar Libya sun taru don halartar jana'izar Saif al-Islam Gaddafi
Harin RSF a wani asibiti a Sudan ya kashe mutum 22, ciki har da ma'aikatan jinya
Ghana da Zambia sun ƙulla yarjejeniyar shiga ƙasashen juna ba tare da biza ba yayin ziyarar Mahama
Saif al-Islam Gaddafi: An kashe ɗan marigayi shugaban Libya Muammar Gaddafi
Afirka na fuskantar tarnaƙin bashin dala biliyan 90 a 2026, in ji S&P
Yadda Biteye na Senegal ke amfani da ƙwallon ƙafa don samun waraka ga ƙwaƙwalwa
Sojojin Rasha sun taimaka wajen daƙile hari a filin jirgin saman Nijar: Moscow
'Yanbindiga sun kashe sojojin Libya uku a kusa da kan iyakar Nijar