| Hausa
AFIRKA
2 minti karatu
Somalia ta musanta satar abincin agaji bayan Trump ya sanar da dakatar da taimako
Amurka ta dakatar da bayar da taimako ga gwamnatin Somaliya bayan wasu rahotanni sun ce hukumomin ƙasar sun "kwace tan 76 ba bisa ƙa’ida ba na abincin da aka bayar na taimako ga masu ƙaramin ƙarfi".
Somalia ta musanta satar abincin agaji bayan Trump ya sanar da dakatar da taimako
Sansani 'yan gudun hijira a Mogadishu da ke Somaliya. / Reuters
21 awanni baya

Somaliya ta musanta zargin cewa jami'ai sun lalata wurin ajiya na Shirin Abinci na Duniya (WFP) kuma sun kwace kayan abinci da Amurka ta dauki nauyi.

Hakan ya biyo bayan dakatar da taimakon da Amurka ta yi wa gwamnatin Somaliya, bayan rahotannin da ke cewa jami'ai sun "kwace tan 76 ba bisa ƙa’ida ba na abincin da aka bayar na taimako ga masu ƙaramin ƙarfi".

A cikin wata sanarwa, ma'aikatar harkokin wajen Somaliya ta ce agajin abincin yana karkashin kulawar Shirin Abinci na Duniya. Ta ce wurin ajiyar da ke cikin yankin tashar jiragen ruwa ta Mogadishu bai tasirantu da ayyukan fadada tashar da ake yi ba.

"Waɗannan ayyuka ba su shafi kulawa, gudanarwa ko rabon agajin jin kai ba," in ji sanarwar.

Gwamnatin Trump ta ce duk wani taimako da za a bayar zai dogara ne kan gwamnatin Somaliya "ta ɗauki alhaki kan ayyukanta da ba za a yarda da su ba kuma ta ɗauki matakan gyara da suka dace," a cewar wani rubutu a shafin sada zumunta na Ma'aikatar Harkokin Waje ta Amurka.

Ma'aikatar Harkokin Wajen Somaliya ta ce damuwar da ake da ita game da zargin kwace agajin jin kai za a warware ta ne ta hannun wani kwamitin hadin gwiwa na hukumomi, kuma gwamnati "ta ci gaba da jajircewa ga gaskiya da ɗaukar alhaki, kuma tana daraja hadin kan ta da Amurka."

A 'yan makonnin da suka gabata Washington ta kai hare-hare sau da yawa kan ‘yan Somaliya da ke Amurka, inda take kai musu hari a wuraren ajiye 'yan gudun hijira a Minnesota, tare da zargin yin babbar zamba kan tallafin jama'a a cikin al'ummar Somaliya na jihar tsakiyar yammacin Amurka — wadda ita ce mafi girma a kasar da kusan mambobi 80,000.

Rumbun Labarai
Shugaban ƙasar Jamhuriyar Tsakiyar Afirka Touadera ya samu nasarar yin wa’adi na uku
Kotun Kolin Guinea ta tabbatar da Doumbouya a matsayin wanda ya lashe zaben kasar
Benin da Nijar sun kori jakadun juna a matakin ramuwar gayya
Sabon rikici ya ɓarke tsakanin sojojin DRC da 'yantawayen M23 a kusa da wani babban gari
Jirgin ruwa ɗauke da ‘yan ci-rani fiye da 200 ya kife a gaɓar tekun Gambia
DRC ta zargi Rwanda da kashe fararen-hula fiye da 1,500 a wata ɗaya da ya gabata
'Ba ma so Isra'ila ta kawo mana matsala,' a cewar shugaban Somalia
Rikicin da ke ta’azzara ya tirsasa wa farar-hula fiye da 4,000 tserewa daga Kordofan a Sudan: MDD
Burkina Faso da Mali sun daina bai wa 'yan Amurka bizar zuwa ƙasashensu
China ta yi Allah wadai da matakin Isra'ila na amincewa da yankin Somaliland
Burhan na Sudan ya yi watsi da yarjejeniya ya ce za a cim ma tsagaita wuta ne bayan janyewar tsageru
Nijeriya ta yi watsi da amincewar da Isra’ila ta yi wa Somaliland a matsayin 'yantacciyar ƙasa
Eritrea ta nemi Kwamitin Tsaro na MDD ya yi martani kan amincewar da Isra'ila ta yi wa Somaliland
Gwamnatin Nijar ta zartar da dokar tilasta wa 'yan ƙasar shiga aikin soja
Mayaƙan RSF kashe mutum 200 a Darfur na Sudan, ciki har da mata da yara: Likitoci
An karrama 'yar sandar da ta ƙi karɓar cin hancin dala 50,000 a Zambiya
Dimokuradiyya ta dawo da ƙarfinta a Somalia bayan shekaru 56
Jamhuriyar Nijar ta dakatar da bai wa 'yan Amurka bizar shiga ƙasarta
Shugaban Burkina Faso Traore ya karɓi ragamar jagorancin ƙungiyar ƙawance ta ƙasashen AES
Zargin almundahanar Naira biliyan ɗaya: Nijeriya na tuhumar Malami da ɗansa da laifuka 16