AFIRKA
2 MINTI KARATU
An kashe mutum 21 a rikicin manoma da makiyaya a Kogi
Wani mazaunin yankin ya ce makiyaya kusan 100 ne suka kai hari a ƙauyensu ranar Alhamis inda suka riƙa yin harbi na kan mai-uwa-da-wabi, yana mai cewa sun gano gawarwaki 19 a lokacin da lamarin ya faru sannan aka gano ƙarin gawawwaki 15 ranar Juma'a.
An kashe mutum 21 a rikicin manoma da makiyaya a Kogi
Wani mazaunin yankin ya ce yawancin mutanen da suka mutu tsofaffi ne da ba za su iya guduwa ba. / Hoto: AP
5 Afrilu 2024

Mutum aƙalla 21 ne suka mutu sakamakon rikicin manoma da makiyaya a jihar Kogi da ke arewa ta tsakiyar Nijeriya, a cewar shaidu.

Edibo Ameh Mark, shugaban ƙaramar hukumar Omala, inda lamarin ya faru, ya ce an binne mutanen da aka kashe.

Ya ƙara da cewa Fulani ne suka kashe mutanen a wani harin ramuwar gayya da suka kai bayan mazauna ƙauyen sun kashe ƴan'uwansu guda shida kwana uku da suka wuce, ciki har da biyu da aka fille wa kawuna.

Rikici tsakanin manoma da makiyaya na ci gaba da barazana a yankin saboda ƙaruwar rashin wuraren kiwo da a wasu lokuta kan sa makiyaya su shiga gonakin al'ummar gari.

"Ba mu taɓa tunanin za a kawo wannan hari ba," in ji Elias Atabo, mai shekara 54. "Maharan sun kwashe fiye da minti 45 suna harbe-harbe."

Wani mazaunin yankin mai suna Atabor Julius ya ce makiyaya kusan 100 ne suka kai hari a ƙauyensu ranar Alhamis inda suka riƙa yin harbi na kan mai-uwa-da-wabi, yana mai cewa sun gano gawarwaki 19 a lokacin da lamarin ya faru sannan aka gano ƙarin gawawwaki 15 ranar Juma'a.

Julius ya ƙara da cewa yawancin mutanen da suka mutu tsofaffi ne da ba za su iya guduwa ba.

Kakakin rundunar ƴan sandan jihar bai ce komai ba game da batun duk da saƙon da aka aika masa.

MAJIYA:TRT Afrika da abokan hulda
Rumbun Labarai
Sojojin Sudan sun harbo jirgi maras matuƙi na RSF a Kordofan ta Arewa
Dakarun Nijar sun cafke muggan makamai da aka yi safararsu daga Libya, sun kama masu safarar ƙwayoyi
RSF ta Sudan ta kai hare-hare a Jihar Khartoum da birnin Atbara bayan amincewa da tsagaita wuta
Paul Biya na Kamaru: Shugaban da ya fi tsufa a duniya ya sha rantsuwar kama aiki karo na takwas
Hatsarin mota ya yi ajalin fiye da mutum 1,000 a Nijar a shekarar 2023, fiye da 12,000 sun jikkata
Sabbin hotunan tauraron dan'adam sun gano alamun 'kaburburan bai-daya a El-Fasher a Sudan
MDD ta yi gargaɗin cewa yaƙin Sudan na gurgunta tattalin arzikin Sudan ta Kudu
Trump ya ce bai kamata Afirka ta Kudu ta kasance cikin G20 ba, ba zai je taronta a Johannesburg ba
'Yan Sudan sun ba da mummunan labarin yi wa mata fyade yayin da suke tserewa daga Al Fasher
An kashe mutane 40 a harin da aka kai wa taron jana'iza a yankin Kordofan na Sudan: MDD
Yadda biranen Afirka mafiya tsafta suke bayyana sauyin da ake samu a nahiyar
Sojojin Ruwa na Ghana sun kama ‘yan Nijeriya 10 da suka ɓuya a jirgin ruwan Panama a Tema
Harin jirgin sama maras matuƙi na RSF ya kashe mutane da dama a lardin Kordofan na Arewa a Sudan
Fiye da mutum 1,500 sun rasa matsugunansu a Sudan sakamakon taɓarɓarewar tsaro: MDD
Dakarun RSF sun kashe mata 300, sun yi wa 25 fyaɗe cikin awa 48 a Al Fasher – Minista
Amurka ta buƙaci a tattauna domin kawo ƙarshen yaƙin Sudan, ba amfani da ƙarfin soja ba
Ana fargabar dubban mutane na cikin 'mummunan hatsari' a birnin Al Fasher na Sudan da RSF ta ƙwace
Shugabar Tanzania Samia Hassan ta lashe zaɓen ƙasar da kashi 97.66 cikin 100
Tchiroma Bakary: Sojojin Kamaru sun yi wa jagoran 'yan adawar kasar rakiya zuwa wuri mai 'aminci'
Kudirin 1325 ya cika shekara 25: Me ya sa dole Afirka ta jagoranci samar da zaman lafiya a duniya