| Hausa
AFIRKA
4 MINTI KARATU
Guinea ta rusa jam'iyyun siyasa da dama na ƙasar
Ba a taɓa ɗaukar irin wannan mataki na rusa jam'iyyun siyasa har guda 53 a tarihin ƙasar Guinea ba wadda ta gudanar da zaɓenta na farko a tsarin dimokuraɗiyya a shekarar 2010 bayan shafe shekaru da dama ana mulkin kama-karya.
Guinea ta rusa jam'iyyun siyasa da dama na ƙasar
  Mamady Doumbouya ya hambarar da Shugaba Alpha Conde a watan Satumba na 2021. / Hoto: Reuters   / Others
29 Oktoba 2024

Mahukunta a ƙasar Guinea sun rusa jam'iyyun siyasa da dama tare da sanya ido kan wasu manyan jam'iyyun adawa biyu a ranar Litinin.

Ƙasar wadda ke Yammacin Afirka tana ƙarkashin mulkin soji ne tun bayan hamɓarar da shugaba Alpha Conde da aka yi shekarar 2021.

Ƙungiyar raya tattalin arzikin kasashen Yammacin Afirka (ECOWAS) ta matsa ƙaimi wajen ganin an dawo da mulkin farar-hula, tare da gudanar da zaɓe a shekarar 2025, sai dai kawo yanzu gwamnatin rikon-ƙwarya ta ƙasar ba ta sanar da lokacin gudanar da zaɓe ba.

Ba a taɓa ɗaukar irin wannan mataki na rusa jam'iyyun siyasa har guda 53 a tarihin ƙasar Guinea ba wadda ta gudanar da zaɓenta na farko a tsarin dimokuraɗiyya a shekarar 2010 bayan shafe shekaru da dama ana mulkin kama-karya.

Ma'aikatar kula da ayyukan yankunan ƙasar ta bayyana wannan sanarwar ce bayan tantance dukkan jam'iyyun siyasar ƙasar da aka soma a watan Yuni.

A cewar ma'aikatar an ɗauki matakin ne domin ''tsaftace harkokin siyasa'' na ƙasar.

Jam'iyyar tsohon shugaban ƙasa

Jam'iyyu 67 da za a sa ido a kan su har na tsawon watanni uku za su ci gaba da yin aiki kamar yadda aka saba amma dole ne su kawar da matsalolin da aka samu a cikin rahoton da aka fitar.

Daga cikin jam'iyyun har da Rally of the Guinean People, jam'iyyar tsohon shugaban ƙasar Alpha Condé, da wata babbar jam'iyyar adawa, Union of Democratic Forces of Guinea.

Hukumomin ƙasar sun ce jam’iyyun da aka sanya ƙarƙashin sa ido sun gaza gudanar da taron jam’iyyarsu a cikin wa’adin da aka ƙayyade tare da ba da bayanan bankinsu da dai sauransu.

Guinea na daya daga cikin ƙasashen Yammacin Afrika masu tasowa ta fuskar ci gaba ciki har Mali, da Nijar da kuma Burkina Faso, waɗanda dukka sojoji suka karɓe mulki tare da jinkirta dawo da mulkin farar-hula.

A farkon wannan shekara ne gwamnatin mulkin soja a Burkina Faso ta tsawaita wa'adin miƙa mulki ga farar-hula da shekaru biyar.

Saɓa alƙawari

Kanar Mamadi Doumbouya wanda ke jagorantar mulkin Guinea, ya yiwa shugaban ƙasar juyin mulki shekaru uku da suka wuce, bayan da ce ya yi ƙoƙarin hana ƙasar faɗawa cikin ruɗani ne tare da ladabtar da gwamnatin da ta shuɗe kan saɓa alƙawari.

Sai dai tun bayan hawansa kan mulki wasu ke sukar sa da cewa bai fi wanda ya gaba daga mulki da komai ba.

A watan Fabrairu, shugaban mulki na sojin ya rusa gwamnatin ba tare da wasu ƙwararan bayanai ba, yana mai cewa za a naɗa wata sabuwa.

Doumbouya ya yi fatali da yunkurin da ƙasashen Yamma da sauran ƙasashe da suka ci gaba ke yi na shiga tsakani a siyasar Afirka da ke fama da kalubale, inda ya ce 'yan Afirka sun gaji da yadda kowa ke ƙoƙarin tsoma baki da abubuwan da suka shafe yankin.''

MAJIYA:AP
Rumbun Labarai
Nijar ta yi tir da 'ɗabi'ar raini' ta Tarayyar Turai kan ƙudurin neman sakin Bazoum
Kenya ta kama ɗan China kan yunƙurin safarar tururuwa fiye da 2,000 da ya ɓoye a cikin kwalabe
Babban birnin Mali Bamako na fuskantar ƙarancin man gas
Kenya ta ƙaddamar da kyamarorin ɗaurawa a jikin jami’an kwastam don yaƙi da rashawa
Umrah 2026: Rufe filin jirgin saman Dubai ya tsayar da sufurin masu zuwa Umrah daga Nijar
Dakarun Nijar sun daƙile harin ta’addanci kan filin jirgin sama na Tahoua
An ji harbe-harbe da ƙarar fashewar wasu abubuwa a yankin Tahoua na Nijar
Ghana ta kai ƙorafi ga MDD bayan makami mai linzami ya jikkata sojojinta a Lebanon
Ɓoyayyiyar matsala a makarantu: Abin da ke jawo wa miliyoyin yara matsalar ji a Afirka
An kashe sojoji 15 a harin 'yanta'adda a Jamhuriyar Benin
Zaftarewar ƙasa ta kashe fiye da mutum 200 a mahaƙar ma'adinai ta Rubaya a Kongo DRC
Rikicin Gabas ta Tsakiya ya tilasta wa jiragen ruwa na duniya sauya hanya suna bi ta Afirka
Gidauniyar Turkiyya ta ba da tallafin abinci ga iyalai 8,250 da iftila’in fari ya shafa a Somaliya
Yaƙin basasa a Sudan na barazana ga ma'aikatan ba da agajin abinci
An gano aƙalla gawawwaki 170 a manyan ƙaburbura a gabashin Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo
Kenya ta kama mutumin da ake zargi da shigar da 'yan ƙasar yaƙin Rasha a Ukraine
Dalilan da suka sa ƙoƙarin samar da ruwa na Afirka ba ya nasara
An kashe 'yanta'adda 17 a Nijar tare da kama masu aikata laifuka da masu taimaka musu 33
Abin da ya sa Afirka ke son a amince da cinikin bayi da mulkin mallaka a matsayin kisan kiyashi
RSF ta kai mummunan hari wani ƙauye a Darfur ta Arewa