| Hausa
DUNIYA
2 minti karatu
An kashe ɗansanda a kusa da Tehran yayin da zanga-zanga kan matsin rayuwa ta mamaye ƙasar Iran
Tun watan da ya gabata zanga-zanga ta mamaye ƙasar Iran saboda tsanantar lalacewar tattalin arziki.
An kashe ɗansanda a kusa da Tehran yayin da zanga-zanga kan matsin rayuwa ta mamaye ƙasar Iran
Protesters march in downtown Tehran, Iran, on December 29, 2025. / Reuters
kwana ɗaya baya

An kashe wani ɗansanda na Iran a wani rikici da ya ɓarke a kusa da babban birnin Tehran, kamar yadda kafofin watsa labarai na cikin gida suka ruwaito a ranar Alhamis.

A cewar rahotanni, an caka wa Laftanar Kanar Shahin Dehghan wuƙa a lokacin zanga-zangar da ta ɓarke a birnin Malard da ke yammacin babban birnin.

Hukumomin tsaro sun ce ana ci gaba da bincike don gano waɗanda ke da hannu a lamarin.

Iran ta fuskanci zanga-zanga tun daga watan jiya wadda ta fara a ranar 28 ga Disamba a babbar kasuwar Tehran, cibiyar harkokin kasuwancin babban birnin, saboda faɗuwar darajar kuɗin Iran da kuma taɓarɓarewar tattalin arziki.

Masu AlakaTRT Afrika - Shin Amurka ta yi nasarar lalata ƙarfin nukiliya na Iran?

Daga baya zanga-zangar ta bazu zuwa birane da dama a faɗin ƙasar.

Hukumomin Iran ba su fitar da alƙaluman waɗanda suka mutu a hukumance ba.

A halin yanzu, kamfanin dillancin labarai na Tasnim ya ce adadin 'yansandan da suka jikkata a lokacin zanga-zangar ya ƙaru zuwa 568, yayin da kuma wasu 'yansanda 66 na rundunar 'yansanda ta Basij su ma suka jikkata.

Iran ta fuskanci zanga-zanga na tsawon makonni a yayin da take fama da taɓarɓarewar tattalin arziki da kuma faɗuwar darajar kuɗin ƙasar, inda kuɗin ƙasar ya ya faɗi zuwa 1,350,000 a matsayin dala ɗaya a kwanan nan.

Rumbun Labarai
Trump ya sanya hannu kan takardar neman cire Amurka daga ƙungiyoyin ƙasa da ƙasa da na MDD
Shugaban Rundunar Sojin Iran ya yi barazanar mayar da martani ga Trump da Netanyahu
Abin da ya sa ya kamata Afirka ta damu kan samamen da Amurka ta kai Venezuela
An sayar da kifi mai nauyin kilogiram 240 a kan Naira biliyan 4.5 ($3.2m) a Japan
Me zai faru ga takunkuman da Amurka ta sanya wa Venezuela bayan ta ɗauke Maduro
Tarayyar Afirka ta nuna 'damuwa', Afirka ta Kudu ta nemi a yi taron MDD da gaggawa kan Venezuela
Trump ya gargaɗi Colombia, ya nufi Cuba bayan ya kama Maduro
Amurka ba za ta bari kowa ya ci gaba daga inda Maduro ya tsaya ba - Trump
Martanin duniya na karuwa kan hare-haren da Amurka ta kai wa Venezuela
An fitar da Shugaba Maduro da matarsa daga Venezuela, in ji Trump
Ƙarar bamabamai ta rikita birnin Caracas bayan Trump ya sha alwashin kai hari a ƙasar Venezuela
Zanga-zangar Iran kan matsin tattalin arziki ta rikiɗe zuwa tashin hankali
Hotuna: Wasan tartsatsin wuta da sauran bukukuwa na maraba da Sabuwar Shekara ta 2026
Fiye da mutum 3,000 ne suka mutu a tafiya ci-rani Turai ta Spain a 2025: Rahoto
Somalia ta yi watsi da amincewar da Isra'ila ta yi wa Somaliland a matsayin barazana ga yankin
Turkiyya ta yi tir da Israila kan amincewa da Somaliland
Kiristoci Falasɗinawa sun gudanar da bukukuwan Kirsimeti a Gaza da Gaɓar Yamma
Rasha na shirin gina tashar nukiliya a duniyar wata nan da shekaru 10 masu zuwa
Babban hafsan sojin Libya da jami'ai sun mutu a hatsarin jirgin sama a kusa da Ankara: Dbeibah
Trump ya saka ƙasashen Afirka biyar cikin jerin da ya haramta wa shiga Amurka