| Hausa
TURKIYYA
2 minti karatu
Turkiyya za ta bai wa 'yan China izinin shiga kasar ba tare da biza ba
Daga ranar 2 ga Janairu, 'yan China za su samu damar zama a Turkiyya har tsawon kwana 90 ba tare biza ba, matakin da zai haɓaka yawon bude ido da cinikayya tsakanin kasashen biyu.
Turkiyya za ta bai wa 'yan China izinin shiga kasar ba tare da biza ba
The visa-free travel for Chinese tourists is expected to further boost people-to-people connections and deepen bilateral relations. / Reuters
1 Janairu 2026

A hukumance Turkiyya ta ba da izinin shiga ba tare da biza ga 'yan kasar China don yawon bude ido da wucewa, kamar yadda dokar shugaban kasar ta bayyana wacce aka wallafa a ranar Laraba.

Sabuwar manufar da Shugaba Recep Tayyip Erdogan ya sanya wa hannu, ta bai wa maziyartan kasar Sin damar zama a Turkiyya na tsawon kwanaki 90 a cikin ko wace kwanaki 180, wacce za ta fara aiki daga ranar 2 ga watan Janairun 2026.

Manufar matakin shi ne karfafa huldar yawon bude ido da kasuwanci tsakanin kasashen biyu, biyo bayan karuwar ‘yan China masu shiga Turkiyya.

Alkaluman kididdiga na kasar Turkiyya sun nuna cewa, a shekarar 2024, masu yawon bude ido ‘yan China 410,000 ne suka ziyarci Turkiyya, wanda ya nuna karuwar kashi 65.1 cikin dari idan aka kwatanta da na shekarar da ta gabata.

Yanzu kasar China ta zama daya daga cikin kasuwannin yawon bude ido na Turkiyya da ke saurin bunkasa.

A farkon wannan shekara, jakadan kasar China ya bayyana irin abubuwan da suke jan hankalin ‘yan China zuwa Turkiyya.

"Dumbin abubuwan tarihi, da al'adu, da abubuwan jan hankali da suka shahara a duniya, su ne suke jan hankalin masu yawon bude ido na China zuwa Turkiyya" in ji shi a wani taron da ya gudana a ofishin jakadancin China da ke Ankara.

"Bayan annobar Korona an ga karuwar masu ziyara, kuma Turkiyya ta zama kasuw mafi saurin bunkasa ga baƙi na duniya."

Jakada Jiang ya yi nuni da cewa, ya shaida dadaddiyar wayewar kasar da abubuwan al'ajabi, yana mai jaddada karuwar huldar al'adu da yawon bude ido a tsakanin kasashen biyu.

Jami'ai na sa ran cewa, ba tare da biza ba, zai kara habaka yawon bude ido 'yan China, da tallafawa tattalin arzikin cikin gida, da ƙarfafa dangantakar dake tsakanin kasashen biyu.

Dangantakar Turkiyya da China na kara karfafa ta hanyar fadada harkokin kasuwanci, yawon bude ido, da mu'amalar al'adu, tare da karfafa hadin gwiwa a fannin tattalin arziki da diflomasiyya.

Rumbun Labarai
Filin jirgin saman Sabiha Gokcen na Istanbul ya karɓi fasinja fiye da miliyan 44 a cikin wata 11
Shugaban Turkiyya ya yi wa Firaiministan Libya ta'aziyya kan mutuwar babban hafsan sojin ƙasar
Turkiyya ta soki ta'addancin RSF a Sudan, ta yi kiran gaggawa don bayar da damar ayyukan jinƙai
Turkiyya ta kai rukunin farko na tantuna 30,000 da za ta kai Sudan a matsayin agaji
Turkiyya za ta ci gaba da fayyace gaskiyar abin da ke faruwa a Gaza: Erdogan
Shirin kawar da shara na Matar Shugaban Turkiyya ya tsara taswirar Ankara na karbar bakuncin COP31
Turkiyya ta kakkaɓo wani jirgi maras matuƙi da ya nufo sararin samaniyarta ta kan Bahar Aswad
Turkiya ta yi Allah wadai da harin da ya kashe sojojin wanzar da zaman lafiya 6 na MDD a Sudan
Turkiyya ta ba da sabbin shawarwari tsaro kan Bahar Aswad bayan ƙaruwar hari kan jiragen ruwa
Saƙon Turkiyya kan Gaza a taron MDD na watan Satumba ya bar Trump cikin tunani: Erdogan
Shugaba Erdogan ya yi gargaɗi kan mayar da Bahar Aswad fagen fama
Turkiyya tana bai wa zaman lafiya da tattaunawa mahimmanci - Shugaba Erdogan
An buɗe Taron Ilimi na Istanbul karo na biyar wanda Gidauniyar Maarif ta shirya
TRT ta fice daga taron EBU a yayin da mahalarta suka yi ce-ce-ku-ce kan shigar Isra'ila Eurovision
Yarjejeniyar zaman lafiya tsakanin Rasha da Ukraine za ta tsara makomar Turai: Fidan na Turkiyya
Turkiyya za ta karɓi baƙuncin manyan tarukan duniya a 2026: Shugaban Erdogan
Jirgin yaƙin Turkiyya maras matuƙi ya kafa tarihin harba wa wani jirgi makami a sararin samaniya
Fafaroma Leo na 14 ya ziyarci Masallacin Sultanahmet da ke Istanbul
An karrama Erdogan da Kambin WHO a Turai saboda ayyukan jinƙan Turkiyya a Falasdinu
A shirye Turkiyya take ta karɓi baƙuncin COP31, da taimakawa don sake gina Gaza: Erdogan