AFIRKA
3 minti karatu
Afirka ta Kudu ta ƙaddamar da butum-butumin malamin makaranta mai amfani da fasahar AI
Butum-tumin mai amfani da na'urar da ake kira IRIS, zai iya amfani da harsunan Afirka ta Kudu ciki har da isiZulu, Afrikaans, Sesotho, da Ingilishi domin koyar da ɗalibai.
Afirka ta Kudu ta ƙaddamar da butum-butumin malamin makaranta mai amfani da fasahar AI
IRIS tana iya magana da harsuna da dama, tana koyar da dukkan darussa daga matakin firamare har zuwa jami'a.
16 Oktoba 2025

Afirka ta Kudu ta shiga sabon zamani na ilimi tare da ƙaddamar da butum-butumi mai koyarwa na farko da ke amfani da fasahar ƙirƙirarriyar basira ta AI. Wannan wata babbar nasara ce a fannin fasaha a nahiyar Afirka.

Jami'ai sun yaba da wannan sabuwar fasaha a matsayin kayan aiki mai sauya yanayin koyarwa a ajujuwa. An sanya wa wannan na'ura suna IRIS, kuma kamfanin BSG Technologies, wani kamfani daga Afirka ta Kudu mai samar da mafita ta fasaha, ne ya ƙirƙire butum-butumin.

IRIS tana iya magana da harsuna da dama, tana koyar da dukkan darussa daga matakin firamare har zuwa jami'a. Tana sadarwa cikin dukkan harsunan hukuma na Afirka ta Kudu, ciki har da isiZulu, Afrikaans, Sesotho, da Ingilishi.

Wanda ya kafa kamfanin, Thandoh Gumede, mai shekaru 31, tsohuwar malama ce daga yankin karkara na Hluhluwe a lardin KwaZulu Natal. Gumede ta bayyana cewa ta fara aiki kan wannan shiri shekaru takwas da suka gabata.

Na'urar koyarwar tana amsa umarnin murya, tana ƙirƙirar yanayin koyarwa mai mu'amala wanda aka tsara don ƙarfafa ɗalibai, musamman a yankunan karkara.

Gumede ta bayyana burinta na kawo wannan na'ura zuwa kowane aji a fadin Afirka ta Kudu, amma ta jaddada cewa hakan zai bukaci haɗin gwiwa da masu haɓaka fasaha da sauran masu ruwa da tsaki.

A lokacin ƙaddamarwa a birnin Durban a watan Agusta, Mataimakiyar Ministan Kimiyya, Fasaha da Kirkire-kirkire na Afirka ta Kudu, Nomalungelo Gina, ta yaba da wannan fasaha a matsayin wata babbar nasara da za ta taimaka wa ɗalibai su cimma cikakken burinsu.

Wasu masu lura da al'amura sun bayyana damuwa cewa shigar na'urorin koyarwa na iya shafar samun aikin malamai a duniya. Duk da haka, jami'an ilimi a Afirka ta Kudu sun bayyana cewa IRIS an tsara ta ne don tallafa wa malamai, ba don maye gurbinsu ba.

Na'urar tana taimakawa wajen bayyana abubuwa masu wahala da kuma tsara darussa bisa ga bukatun ɗalibai, yayin da malamai ke samun horo don aiki tare da ita. A lokacin gwajin na'urar, IRIS ta bayyana wani ra'ayi mai wahala na lissafi cikin sauƙi, wanda ya samu gagarumar yabo.

Mataimakiyar Minista Nomalungelo ta yi kira ga mata da matasa su shiga fannin fasahar AI, tana bayyana waɗannan ƙwarewar a matsayin manyan abubuwan da ke tafiyar da tattalin arziki.

Ma'aikatar Ilimi ta Afirka ta Kudu ta yaba da IRIS a matsayin misali na yadda ƙirƙire-ƙirƙire da matasa suka jagoranta za su iya haɓaka ci gaban ƙasa. Duk da cewa ana sa ran aiwatar da wannan fasaha a hankali a fadin ƙasar, ƙaddamarwar ta nuna wani babban mataki zuwa makomar ilimi mai amfani da fasahar wucin-gadi a Afirka ta Kudu da ma nahiyar baki ɗaya.

Rumbun Labarai
Paul Biya na Kamaru: Shugaban da ya fi tsufa a duniya ya sha rantsuwar kama aiki karo na takwas
Hatsarin mota ya yi ajalin fiye da mutum 1,000 a Nijar a shekarar 2023, fiye da 12,000 sun jikkata
Sabbin hotunan tauraron dan'adam sun gano alamun 'kaburburan bai-daya a El-Fasher a Sudan
MDD ta yi gargaɗin cewa yaƙin Sudan na gurgunta tattalin arzikin Sudan ta Kudu
Trump ya ce bai kamata Afirka ta Kudu ta kasance cikin G20 ba, ba zai je taronta a Johannesburg ba
'Yan Sudan sun ba da mummunan labarin yi wa mata fyade yayin da suke tserewa daga Al Fasher
An kashe mutane 40 a harin da aka kai wa taron jana'iza a yankin Kordofan na Sudan: MDD
Yadda biranen Afirka mafiya tsafta suke bayyana sauyin da ake samu a nahiyar
Sojojin Ruwa na Ghana sun kama ‘yan Nijeriya 10 da suka ɓuya a jirgin ruwan Panama a Tema
Harin jirgin sama maras matuƙi na RSF ya kashe mutane da dama a lardin Kordofan na Arewa a Sudan
Fiye da mutum 1,500 sun rasa matsugunansu a Sudan sakamakon taɓarɓarewar tsaro: MDD
Dakarun RSF sun kashe mata 300, sun yi wa 25 fyaɗe cikin awa 48 a Al Fasher – Minista
Amurka ta buƙaci a tattauna domin kawo ƙarshen yaƙin Sudan, ba amfani da ƙarfin soja ba
Ana fargabar dubban mutane na cikin 'mummunan hatsari' a birnin Al Fasher na Sudan da RSF ta ƙwace
Shugabar Tanzania Samia Hassan ta lashe zaɓen ƙasar da kashi 97.66 cikin 100
Tchiroma Bakary: Sojojin Kamaru sun yi wa jagoran 'yan adawar kasar rakiya zuwa wuri mai 'aminci'
Kudirin 1325 ya cika shekara 25: Me ya sa dole Afirka ta jagoranci samar da zaman lafiya a duniya
Dubban mutane sun tsere daga North Kordofan yayin da RSF ta zafafa kai hari a yankin Darfur na Sudan
Fararen-hula 177,000 sun maƙale a Al Fasher na Sudan, yayin da RSF ke ci gaba da kisa - Likitoci
Rundunar RSF ta amsa aikata 'take haƙƙi' a Al Fasher na Sudan