| hausa
AFIRKA
2 minti karatu
Mutum 12 sun mutu a turmutsutsun neman aikin soja a Ghana – Rahotanni
Tun da fari a sanarwar da ta fitar, Rundunar Tsaro ta Ghana, GAF ta ce mutum shida ne suka mutu a wajen jarabawar neman aikin da aka yi ranar Laraba, 11 ga watan Nuwamban 2025.
Mutum 12 sun mutu a turmutsutsun neman aikin soja a Ghana – Rahotanni
Mutum 12 sun mutu  a turmutsutsun neman aikin soja a Ghana – Rahotanni
12 Nuwamba 2025

Rahotanni daga Ghana sun ce mutum 12 sun rasa rayukansu sannan wasu da dama sun jikkata a wani turmutsutsu da ya faru yayin jarabawar daukar aiki ta sojoji a Filin Wasa na El-Wak da ke Accra, babban birnin kasar.

Tun da fari a sanarwar da ta fitar, Rundunar Tsaro ta Ghana, GAF ta ce mutum shida ne suka mutu a wajen jarabawar neman aikin da aka yi ranar Laraba, 11 ga watan Nuwamban 2025.

Sanarwar ta ce lamarin ya faru ne da misalin karfe 6.20 na safe agogon kasar, a yayin da dumbin masu neman aikin suka take tsarin shiga wajen inda suka kutsa ba a cikin tsari ba, kafin lokacin fara jarabawar ya yi.

‎Sanarwar ta ce mutum shida sun rasa rayukansu, yayin da wasu da dama suka jikkata a turmutsutsun. A yanzu haka wadanda suka ji rauni na asibitin sojoji ana kula da su.

Amma rahotanni sun ce yawan wadanda suka mutun ya karu zuwa 12.

‎”Rundunar Tsaron Ghana tana bai wa al’umma tabbacin cewa tawagogin lafiya suna aiki ba gajiyawa don kula da wadanda abin ya shafa,” in ji sanarwar, tana mai cewa ana kuma shirye-shiryen sanar da iyalan wadanda suka rasu batun.

Rundunar TSaron Ghana ta mika sakon jaje da na ta’azziyarta ga iyalan wadanda suka rasu da kuma fatan samun sauki ga marasa lafiya.

 

Rumbun Labarai
UN Women: Mata da 'yan mata 11M suna fama da matsanancin ƙarancin abinci a Sudan sakamakon yaƙi
WHO ta bayyana damuwa kan karuwar masu ciwon siga a Afirka
Kisan kare dangi a boye da bayyane: Gushewar jinkai a Al Fasher
An ba da belin dan Gaddafi bayan da ya shafe shekaru 10 a tsare a Lebanon
Gwamnatin Trump 'ta aika wa Equatorial Guinea dala miliyan 7.5' don ta karɓi waɗanda Amurka ta kora
Ƙasashe fiye da 20 sun yi Allah wadai da RSF kan kashe-kashen da take yi a Sudan
Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya ya yi kira da a dakatar da zubar da jini a Sudan
Paul Biya na Kamaru: Dan siyasar da zai ci gaba da yin mulki har sai ya kai shekara 99?
Hare-haren RSF sun kori ƙarin dubban mutane daga Darfur da Kordofan na Sudan
RSF ta binne gawawwaki a kabarin bai-ɗaya, ta ƙone wasu domin 'ɓoye laifukan yaƙi': Likitocin Sudan
Sojojin Sudan sun harbo jirgi maras matuƙi na RSF a Kordofan ta Arewa
Dakarun Nijar sun cafke muggan makamai da aka yi safararsu daga Libya, sun kama masu safarar ƙwayoyi
RSF ta Sudan ta kai hare-hare a Jihar Khartoum da birnin Atbara bayan amincewa da tsagaita wuta
Paul Biya na Kamaru: Shugaban da ya fi tsufa a duniya ya sha rantsuwar kama aiki karo na takwas
Hatsarin mota ya yi ajalin fiye da mutum 1,000 a Nijar a shekarar 2023, fiye da 12,000 sun jikkata
Sabbin hotunan tauraron dan'adam sun gano alamun 'kaburburan bai-daya a El-Fasher a Sudan
MDD ta yi gargaɗin cewa yaƙin Sudan na gurgunta tattalin arzikin Sudan ta Kudu
Trump ya ce bai kamata Afirka ta Kudu ta kasance cikin G20 ba, ba zai je taronta a Johannesburg ba
'Yan Sudan sun ba da mummunan labarin yi wa mata fyade yayin da suke tserewa daga Al Fasher
An kashe mutane 40 a harin da aka kai wa taron jana'iza a yankin Kordofan na Sudan: MDD