| Hausa
DUNIYA
2 minti karatu
An katse intanet da wayoyin hannu a Iran
Kungiyar sanya idanu ta NetBlocks ta ce alkaluma sun nuna Iran na fuskantar katsewar internet a fadin kasar.
An katse intanet da wayoyin hannu a Iran
Wata kungiyar kare hakkin dan adam da ke sa ido kan Iran ta ba da rahoton cewa masu zanga-zanga da dama sun mutu. / Reuters
16 awanni baya

Iran na fuskantar katsewar intanet a faɗin ƙasar, inda rahotanni ke nuna cewa an katse ayyukan sadarwa da amfani da wayar hannu.

"Bayanai na kai-tsaye sun nuna cewa a yanzu Iran tana cikin tsakiyar katsewar intanet a dukka faɗin ƙasar," in ji ƙungiyar sa ido kan intanet ta NetBlocks da ke Landan a wata sanara ta shafin X a ranar Alhamis.

Rahotannin kafofin watsa labarai sun ce an katse ayyukan wayar hannu jim kaɗan bayan rufe intanet, ko da yake hukumomin Iran ba su fitar da wata sanarwa a hukumance ba.

An ruwaito cewa katsewar ta biyo bayan gudanar da zanga-zanga a Iran tun daga ƙarshen Disamba, wanda ke da alaƙa da faɗuwar darajar kuɗin ƙasar da kuma ƙalubalen tattalin arziki da ke ci gaba da fuskantar ƙasar.

Adadin waɗanda suka mutu sakamakon zanga-zangar da ake yi a Iran ya ƙaru zuwa 38, kamar yadda wata ƙungiyar kare hakkin ɗan’adam da ta mayar da hankali kan Iran ta ruwaito a ranar Laraba.

Zanga-Zanga ta bazu a fadin kasar

Iran ta fuskanci zanga-zanga mai yawa tun daga watan da ya gabata, wadda aka fara daga ranar 28 ga Disamba a babbar kasuwar Tehran, saboda raguwar darajar kuɗin Iran da kuma taɓarɓarewar tattalin arziki.

Daga baya zanga-zangar ta bazu zuwa wasu birane da dama a faɗin ƙasar.

Wata ƙungiyar kare hakkin ɗan’adam da ke sa ido kan Iran ta ba da rahoton cewa masu zanga-zanga da dama sun mutu.

Hukumomin Iran ba su tabbatar da adadin waɗanda suka mutu ba ko kuma sun bayar da cikakkun bayanai game da waɗanda suka mutu ko suka jikkata.

Ma'aikatar Harkokin Wajen Iran a ranar Laraba ta yi Allah wadai da "shisshigi a harkokin cikin gidan Iran" da Amurka ta yi a tsaka da zanga-zangar da ake yi a birane daban-daban.

Tehran ta jaddada a cikin wata sanarwa a shafin intanet na Ma'aikatar Harkokin Wajen cewa Amurka "tana da ƙiyayya ga al'ummar Iran" kuma ta yi Allah wadai da abin da ta bayyana a matsayin ɗabi'u da manufofin Amurka game da Iran.

 

Rumbun Labarai
Trump ya sanya hannu kan takardar neman cire Amurka daga ƙungiyoyin ƙasa da ƙasa da na MDD
Shugaban Rundunar Sojin Iran ya yi barazanar mayar da martani ga Trump da Netanyahu
Abin da ya sa ya kamata Afirka ta damu kan samamen da Amurka ta kai Venezuela
An sayar da kifi mai nauyin kilogiram 240 a kan Naira biliyan 4.5 ($3.2m) a Japan
Me zai faru ga takunkuman da Amurka ta sanya wa Venezuela bayan ta ɗauke Maduro
Tarayyar Afirka ta nuna 'damuwa', Afirka ta Kudu ta nemi a yi taron MDD da gaggawa kan Venezuela
Trump ya gargaɗi Colombia, ya nufi Cuba bayan ya kama Maduro
Amurka ba za ta bari kowa ya ci gaba daga inda Maduro ya tsaya ba - Trump
Martanin duniya na karuwa kan hare-haren da Amurka ta kai wa Venezuela
An fitar da Shugaba Maduro da matarsa daga Venezuela, in ji Trump
Ƙarar bamabamai ta rikita birnin Caracas bayan Trump ya sha alwashin kai hari a ƙasar Venezuela
Zanga-zangar Iran kan matsin tattalin arziki ta rikiɗe zuwa tashin hankali
Hotuna: Wasan tartsatsin wuta da sauran bukukuwa na maraba da Sabuwar Shekara ta 2026
Fiye da mutum 3,000 ne suka mutu a tafiya ci-rani Turai ta Spain a 2025: Rahoto
Somalia ta yi watsi da amincewar da Isra'ila ta yi wa Somaliland a matsayin barazana ga yankin
Turkiyya ta yi tir da Israila kan amincewa da Somaliland
Kiristoci Falasɗinawa sun gudanar da bukukuwan Kirsimeti a Gaza da Gaɓar Yamma
Rasha na shirin gina tashar nukiliya a duniyar wata nan da shekaru 10 masu zuwa
Babban hafsan sojin Libya da jami'ai sun mutu a hatsarin jirgin sama a kusa da Ankara: Dbeibah
Trump ya saka ƙasashen Afirka biyar cikin jerin da ya haramta wa shiga Amurka