| hausa
GABAS TA TSAKIYA
2 minti karatu
Israila ta rushe gidajen Falasɗinawa a Gaza, ta ƙaddamar da sabon hari a Khan Younis
Sojojin mamaya na Isra’ila na ci gaba da rushe gidaje a unguwar Zeitoun, yayin da motocin soji ke luguden wuta sosai a gabashin birnin, kuma nau'uka daban-daban na jiragen sama marasa matuƙa na shawagi a yankin yammacin birnin.
Israila ta rushe gidajen Falasɗinawa a Gaza, ta ƙaddamar da sabon hari a Khan Younis
Yawancin rushe-rushen ana aiwatar da su ne a gaban wurin da aka shata “layin rawaya,” a cikin yankin da sojojin Isra’ila suka mamaye.
10 Nuwamba 2025

Sojojin Isra’ila na ci gaba da rushe gidajen Falasɗinawa a unguwar Zeitoun da ke kudu maso gabashin birnin Gaza, yayin da suke kuma kai hare-hare ta sama masu ƙarfi kan birnin Khan Younis a kudu.

Sojojin mamaya na Isra’ila na ci gaba da rushe gidaje a unguwar Zeitoun, yayin da motocin soji ke luguden wuta sosai a gabashin birnin, kuma nau'uka daban-daban na jiragen sama marasa matuƙa na shawagi a yankin yammacin birnin.

Jiragen yaƙi na Isra’ila na kuma kai hare-haren sama masu tsanani a yankunan arewa da gabashin Khan Younis, yayin da aka harba makaman atilari na Isra’ila suka harba wasu bamabamai a yankin Zanna, da ke arewa maso gabashin birnin.

Yawancin rushe-rushen ana aiwatar da su ne a gaban wurin da aka shata “layin rawaya,” a cikin yankin da sojojin Isra’ila suka mamaye.

“Layin rawaya” na nufin yankin da sojojin Isra’ila suka janye zuwa gare shi bisa yarjejeniyar tsagaita wuta da ta fara aiki a ranar 10 ga Oktoba. Layi ne wanda ido bai iya gani wanda ya ratsa Gaza sannan ya raba yankin na Falasɗinawa gida biyu.

Adadin waɗanda suka mutu ya ƙaru zuwa 241, yayin da wasu 619 suka jikkata, kuma an ciro gawawwaki 528.

Wannan ya sa jimillar adadin mutanen da suka mutu tun lokacin da Isra’ila ta fara yaƙin kisan kare dangi a Gaza a 7 ga Oktoban 2023 ya kai 69,176 sai kuma mutum 170,690 suka jikkata.

Rumbun Labarai
Hare-haren Isra'ila a Gaza sun kashe mutane 91, ciki har da yara 24, duk da tsagaita wuta
Netanyahu ya ba da umarnin a kai 'hare-hare masu karfi' kan Gaza
Shin Trump zai yanke alaka da Isra'ila idan ta ci gaba da mamaye Gabar Yammacin Kogin Jordan?
Amurka ta tsare ɗan jaridar Birtaniya Musulmi mai suna Sami Hamdi saboda sukar Isra'ila
Fiye da tan miliyan 61 na tarkace da baraguzai sun rufe Gaza a shekara biyu na yakin Isra'ila: UNRWA
Kalaman Trump na lalata cibiyoyin nukiliyar Iran 'mafarki ne': Khamenei
Wata ƙungiyar bayar da agaji ta Turkiyya ta ƙaddamar aikin kwashe ɓaraguzai a arewacin Gaza
Sojojin Israila sun buɗe wuta kan wasu manoma Falasɗinawa a yayin da suke girbe zaitun a Gaɓar Yamma
Mene ne abu na gaba a shirin zaman lafiya na Gaza?
Isra'ila ta sake buɗe mashigar Rafah don bai wa manyan motocin kayan agaji damar shiga Gaza
Turkiyya, Masar, Qatar da Amurka sun sa hannu kan takardar yarjejeniyar tsagaita wuta ta Gaza
Dauwamammen zaman lafiya zai samu ne kawai ta hanyar kafa ƙasashe biyu, Erdogan ya faɗa wa Starmer
Sojojin Hamas sun kashe mutum 32 cikin 'gungun' da ke sace kayan agaji a Gaza
Hamas ta kammala sakin 'yan Isra'ila 20 da ta tsare a matakin farko na yarjejeniyar tsagaita wuta
Wani bidiyo ya nuna yadda Isra'ila ke cin zarafin fursunonin Falasɗinawa gabanin sakin su
Trump, Sisi za su jagoranci taron zaman lafiya kan Gaza a birnin Sharm el-Sheikh a ranar Litinin
Sojojin Amurka sun isa Isra'ila domin sa ido kan aiwatar da yarjejeniyar tsagaita wuta ta Gaza
Sojojin Isra'ila sun fara janyewa a hankali zuwa gabashin Gaza: Kafofin watsa labarai
Gwamnatin Isra’ila ta amince da yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza ta Trump
Shekaru biyu na kisan kiyashin Isra'ila a Gaza: Falasdinawa suna shan yunwa da cin-amana