| Hausa
DUNIYA
3 minti karatu
Erdogan da Anwar na son ƙarfafa alaƙar Turkiyya da Malaysia tare da fifita fannin tsaro
Shugabannin biyu sun yaba wa kamannin juna da ƙarfin fasahar ƙere-ƙerensu a yayin da Ankara da Kuala Lumpur ke zurfafa dabaru da dangantar tattalin arziki.
Erdogan da Anwar na son ƙarfafa alaƙar Turkiyya da Malaysia tare da fifita fannin tsaro
Firaministan Malaysia Anwar ya yaba da fasahar kere-kere ta Turkiyya, / AA
8 Janairu 2026

Shugaba Recep Tayyip Erdogan ya ce Turkiyya za ta ci gaba da auna matakan haɗin gwiwa da Malaysia a fannin tsaro a ƙarƙashin tsarin "kowa ya amfana", yayin da ƙasashen biyu ke neman faɗaɗa haɗin gwiwa a fannoni daban-daban na dabaru, tattalin arziki, da kuma diflomasiyya.

Da yake jawabi a wani taron manema labarai na haɗin gwiwa a Ankara tare da Firaministan Malaysia Anwar Ibrahim a ranar Laraba, Erdogan ya ce an gudanar da taron haɗin gwiwa na farko na manyan jami'ai - wanda aka amince da shi a lokacin ziyararsa a Kuala Lumpur a bara - wanda hakan ke nuna wani mataki na zahiri na haɗin gwiwa tsakanin ƙasashen biyu.

Erdogan ya kuma yi kira ga Malaysia da ta faɗaɗa zuba jarinta a Turkiyya, yana mai nuni da ƙaruwar damarmaki a fannin tsaro, ababen more rayuwa, da kuma manyan masana'antu.

Erdogan “Shugaba ne mai girma”

A nasa ɓangaren, Anwar ya yaba da fasahar ƙere-ƙere ta Turkiyya, yana mai yaba wa "ikon al'ummar Turkiyya da masana'antu a fannin kimiyya da fasaha," kuma ya ce Malaysia na kallon Turkiyya a matsayin abokiyar hulɗa mai muhimmanci a ci gaban da ke da alaƙa da ƙirƙire-ƙirƙire.

Anwar ya kuma gode wa Erdogan saboda abin da ya bayyana a matsayin "jagorancinsa mai jarumtaka ba kawai ga Turkiyya ba har ma ga duniya baki ɗaya, musamman ga duniyar Musulmi," wanda ke nuna kyakkyawan daidaiton siyasa tsakanin shugabannin biyu.

Baya ga tsaro da zuba hannun jari, Erdogan ya ce tattaunawar ta shafi ilimi, al'adu da alaƙar mutane, yana mai bayyana su a matsayin ginshiƙai na haɗin gwiwa na dogon lokaci.

"Mun kuma yi shawarwari kan batun bil’adama wanda ke samar da tushen abota da 'yan'uwantaka tsakanin Turkiyya da Malaysia," in ji Erdogan.

"Mun yanke shawarar ci gaba da ƙoƙarinmu a fannin ilimi, raya al'adu, da yawon buɗe ido, da kuma ɗaukar matakan da za su ƙarfafa tattaunawa tsakanin al'ummominmu," in ji shi.

An kuma tattauna batutuwan yanki da na duniya, inda ɓangarorin biyu suke da ra’ayi da matsaya iri guda.

"Musamman, za mu ci gaba da bin diddigin Gaza sosai," in ji Erdogan, yana mai jaddada damuwa game da rikicin yankin.

Shugaban Turkiyya ya ƙara da cewa Ankara ta bayar da muhimmanci ga hulɗa da abokanta na yankin da kuma ASEAN a ƙarƙashin shirinta na ‘Asia Anew’, wanda aka ƙaddamar a shekarar 2019, kuma ta yaba da ƙoƙarin Anwar na taimaka wa wajen rage tashin hankali tsakanin Thailand da Cambodia.

 

Rumbun Labarai
Trump ya sanya hannu kan takardar neman cire Amurka daga ƙungiyoyin ƙasa da ƙasa da na MDD
Shugaban Rundunar Sojin Iran ya yi barazanar mayar da martani ga Trump da Netanyahu
Abin da ya sa ya kamata Afirka ta damu kan samamen da Amurka ta kai Venezuela
An sayar da kifi mai nauyin kilogiram 240 a kan Naira biliyan 4.5 ($3.2m) a Japan
Me zai faru ga takunkuman da Amurka ta sanya wa Venezuela bayan ta ɗauke Maduro
Tarayyar Afirka ta nuna 'damuwa', Afirka ta Kudu ta nemi a yi taron MDD da gaggawa kan Venezuela
Trump ya gargaɗi Colombia, ya nufi Cuba bayan ya kama Maduro
Amurka ba za ta bari kowa ya ci gaba daga inda Maduro ya tsaya ba - Trump
Martanin duniya na karuwa kan hare-haren da Amurka ta kai wa Venezuela
An fitar da Shugaba Maduro da matarsa daga Venezuela, in ji Trump
Ƙarar bamabamai ta rikita birnin Caracas bayan Trump ya sha alwashin kai hari a ƙasar Venezuela
Zanga-zangar Iran kan matsin tattalin arziki ta rikiɗe zuwa tashin hankali
Hotuna: Wasan tartsatsin wuta da sauran bukukuwa na maraba da Sabuwar Shekara ta 2026
Fiye da mutum 3,000 ne suka mutu a tafiya ci-rani Turai ta Spain a 2025: Rahoto
Somalia ta yi watsi da amincewar da Isra'ila ta yi wa Somaliland a matsayin barazana ga yankin
Turkiyya ta yi tir da Israila kan amincewa da Somaliland
Kiristoci Falasɗinawa sun gudanar da bukukuwan Kirsimeti a Gaza da Gaɓar Yamma
Rasha na shirin gina tashar nukiliya a duniyar wata nan da shekaru 10 masu zuwa
Babban hafsan sojin Libya da jami'ai sun mutu a hatsarin jirgin sama a kusa da Ankara: Dbeibah
Trump ya saka ƙasashen Afirka biyar cikin jerin da ya haramta wa shiga Amurka