| Hausa
AFIRKA
1 minti karatu
Nijar ta soke ayyukan ɗaruruwan ƙungiyoyi masu zaman kansu na cikin gida da na ƙasashen waje
Ma’aikatar Harkokin Cikin Gida ta Nijar ɗin ce ta soke ayyukan ƙungiyoyin sakamakon rashin bin ƙa’idojin aiki musamman rashin gabatar da takardunsu na ayyuka a lokacin da gwamnatin ƙasar ke duba ayyukansu, in ji gwamnatin ƙasar.
Nijar ta soke ayyukan ɗaruruwan ƙungiyoyi masu zaman kansu na cikin gida da na ƙasashen waje
A halin yanzu ƙungiyoyi 1,809 ne kawai suka cika sharuɗan da suka dace domin ci gaba da gudanar da ayyukansu a ƙasar.
18 awanni baya

Gwamnatin Nijar ta soke ayyukan ƙungiyoyi masu zaman kansu da dama a ƙasar.

Ma’aikatar Harkokin Cikin Gida ta Nijar ɗin ce ta soke ayyukan ƙungiyoyin sakamakon rashin bin ƙa’idojin aiki musamman rashin gabatar da takardunsu na ayyuka a lokacin da gwamnatin ƙasar ke duba ayyukansu a tsakanin 14 zuwa 15 ga Nuwambar 2015 duk da sanar da su da aka yi game da hakan, kamar yadda ma’aikatar ta tabbatar.

A cikin fiye da ƙungiyoyi masu zaman kansu fiye da 3,000, ƙungiyoyi 1,684 na ƙasar ne kaɗai suka cika sharuɗa sai kuma ƙungiyoyin ƙasa da ƙasa 125 ne suka cika sharuɗan.

A halin yanzu ƙungiyoyi 1,809 ne kawai suka cika sharuɗan da suka dace domin ci gaba da gudanar da ayyukansu a ƙasar.

Gwamnatin ta Nijar ta ce ta wallafa cikakkun sunayen duka ƙungiyoyin da suka cancanta su ci gaba da gudanar da ayyukansu a ƙasar a cikin takardun dokar da gwamnatin ƙasar ta yi.