| Hausa
AFIRKA
1 minti karatu
Nijar ta soke ayyukan ɗaruruwan ƙungiyoyi masu zaman kansu na cikin gida da na ƙasashen waje
Ma’aikatar Harkokin Cikin Gida ta Nijar ɗin ce ta soke ayyukan ƙungiyoyin sakamakon rashin bin ƙa’idojin aiki musamman rashin gabatar da takardunsu na ayyuka a lokacin da gwamnatin ƙasar ke duba ayyukansu, in ji gwamnatin ƙasar.
Nijar ta soke ayyukan ɗaruruwan ƙungiyoyi masu zaman kansu na cikin gida da na ƙasashen waje
A halin yanzu ƙungiyoyi 1,809 ne kawai suka cika sharuɗan da suka dace domin ci gaba da gudanar da ayyukansu a ƙasar.
10 Janairu 2026

Gwamnatin Nijar ta soke ayyukan ƙungiyoyi masu zaman kansu da dama a ƙasar.

Ma’aikatar Harkokin Cikin Gida ta Nijar ɗin ce ta soke ayyukan ƙungiyoyin sakamakon rashin bin ƙa’idojin aiki musamman rashin gabatar da takardunsu na ayyuka a lokacin da gwamnatin ƙasar ke duba ayyukansu a tsakanin 14 zuwa 15 ga Nuwambar 2015 duk da sanar da su da aka yi game da hakan, kamar yadda ma’aikatar ta tabbatar.

A cikin fiye da ƙungiyoyi masu zaman kansu fiye da 3,000, ƙungiyoyi 1,684 na ƙasar ne kaɗai suka cika sharuɗa sai kuma ƙungiyoyin ƙasa da ƙasa 125 ne suka cika sharuɗan.

A halin yanzu ƙungiyoyi 1,809 ne kawai suka cika sharuɗan da suka dace domin ci gaba da gudanar da ayyukansu a ƙasar.

Gwamnatin ta Nijar ta ce ta wallafa cikakkun sunayen duka ƙungiyoyin da suka cancanta su ci gaba da gudanar da ayyukansu a ƙasar a cikin takardun dokar da gwamnatin ƙasar ta yi.

 

 

Rumbun Labarai
Harin RSF na watan Oktoban 2025 a Al-Fasher na Sudan ya kashe aƙalla mutum 6,000: Rahoton MDD
AU: Shugabannin Afirka sun ƙaddamar da taron Ƙungiyar Tarayyar Afirka da batun ruwa da sauyin yanayi
Afirka ce kan-gaba wajen faɗaɗa samar da lantarki ta hasken rana a shekarar 2025: Rahoto
Gwamnatin Ghana ta ba da umarnin sarrafa kashi 50 cikin 100 na koko a cikin ƙasar
Sudan: Aƙalla mutum 21 sun mutu a hatsarin kwale-kwale a Kogin Nilu
Kasashe shida sun shiga Kwamitin Tsaro na Tarayyar Afirka
RSF ta kashe ƙananan yara a harin da ta kai wani masallaci a yankin Kordofan na Sudan
Saudiyya ta yi tur da RSF kan munanan ayyukanta a Al Fasher, ta buƙaci a ba da hanyar kai agaji
Mutum biyar sun mutu a hatsarin helikwaftan ɗaukar marasa lafiya a Libya
Yadda 'yan Somaliya suka gina wa tsohon shugaba ƙasarsu Farmaajo sabon gida
Sake dawo da ainihin martabar Afirka
RSF ta Sudan ta kai hari da jirgi maras matuƙi, ta kashe gomman mutane da yara
Dubban ‘yan kasar Libya sun taru don halartar jana'izar Saif al-Islam Gaddafi
Harin RSF a wani asibiti a Sudan ya kashe mutum 22, ciki har da ma'aikatan jinya
Ghana da Zambia sun ƙulla yarjejeniyar shiga ƙasashen juna ba tare da biza ba yayin ziyarar Mahama
Saif al-Islam Gaddafi: An kashe ɗan marigayi shugaban Libya Muammar Gaddafi
Afirka na fuskantar tarnaƙin bashin dala biliyan 90 a 2026, in ji S&P
Yadda Biteye na Senegal ke amfani da ƙwallon ƙafa don samun waraka ga ƙwaƙwalwa
Sojojin Rasha sun taimaka wajen daƙile hari a filin jirgin saman Nijar: Moscow
'Yanbindiga sun kashe sojojin Libya uku a kusa da kan iyakar Nijar