| hausa
AFIRKA
2 minti karatu
Sojojin Sudan sun daƙile harin RSF kan filin jirgin sama da dam a arewacin ƙasar
Bayan mayaƙan RSF sun ƙwace Al Fasher, sun mayar da hankali wurin yin arangama da sojojin Sudan a wasu sabbin wurare.
Sojojin Sudan sun daƙile harin RSF kan filin jirgin sama da dam a arewacin ƙasar
Yadda baƙin hayaƙi ke tashi daga wata ma'ajiyar fetur bayan mayaƙan RSF suka kai hari a Port Sudan, ranar 5 ga Mayun 2025.
5 awanni baya

Sojojin Sudan ranar Alhamis sun daƙile wani hari na jirgi maras matuƙi da mayaƙan Rapid Support Forces (RSF) suka kai a wasu mahimman wurare, ciki har da filin jirgin sama da wata madatasar ruwa a arewacin ƙasar.

Runduna ta 19 ta sojojin ƙasar ta bayyana a wata sanarwa cewa dakarunta sun daƙile wasu jirage marasa matuƙa na ƙunar-baƙin-wake da RSF ta tura da safiyar Alhamis a wani yunƙuri na kai hari a hedkwatar rundunar da filin jiragen sama na Merowe da kuma dam ɗin Merowe a jihar ta Northern State.

An ji ƙarar ababe masu fashewa a harabar filin jiragen saman da dam ɗin, kamar yadda shaidu suka bayyana wa kafar yada labaram Sudan News ta ƙasar. Ba a dai gane iyakar ɓarnar da harin ya yi ba.

Babu wani tsokaci nan take daga rundunar RSF game da sanarwar da sojin ƙasar ta fitar.

A matsayin ɗaya daga cikin mahimman wurare a arewacin Sudan, Merowe ya ƙunshi wani filin jiragen sama da ake amfani da shi domin buƙatu na soji da na fararen-hula tare da dam ɗin Merowe, ɗaya daga cikin ababen more rayuwa da suka fi girma a ƙasar.

Al-Rakoba News, wadda ta ambato majiyoyi na cikin gida, ta ce harin ya kuma mayar da hankali kan babban birnin Jihar Dongola da kuma birnin Al-Dabba.

Bayan RSF ta ƙwace Al Fasher, babban birnin Jihar North Darfur, arangama tsakanin ƙungiyar da sojin Sudan ta bazu zuwa sabbin wuraren yaƙi, musamman jihohin tsakiya da kudancin Kordofan.

Daga cikin jihohin Sudan 18, a halin yanzu rundunar RSF tana riƙe da dukkan jihohi biyar na yankin Darfur, face wasu yankunan arewaci kaɗan na North Darfur wadanda har yanzu ke ƙarƙashin ikon soji.

Sojin Sudan na ci gaba da mamaye yawancin sauran jihohi 13 a yankunan kudanci da arewa da gabashi da kuma tsakiya ciki har da babban birnin ƙasar Khartoum.

Rikicin na zub da jini tsakanin soji da RSF, wanda aka fara a watan Afrilun shekarar 2023, ya kashe dubban mutane tare da raba miliyoyin mutane da gidajensu.

Rumbun Labarai
UN Women: Mata da 'yan mata 11M suna fama da matsanancin ƙarancin abinci a Sudan sakamakon yaƙi
WHO ta bayyana damuwa kan karuwar masu ciwon siga a Afirka
Kisan kare dangi a boye da bayyane: Gushewar jinkai a Al Fasher
An ba da belin dan Gaddafi bayan da ya shafe shekaru 10 a tsare a Lebanon
Gwamnatin Trump 'ta aika wa Equatorial Guinea dala miliyan 7.5' don ta karɓi waɗanda Amurka ta kora
Ƙasashe fiye da 20 sun yi Allah wadai da RSF kan kashe-kashen da take yi a Sudan
Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya ya yi kira da a dakatar da zubar da jini a Sudan
Paul Biya na Kamaru: Dan siyasar da zai ci gaba da yin mulki har sai ya kai shekara 99?
Hare-haren RSF sun kori ƙarin dubban mutane daga Darfur da Kordofan na Sudan
RSF ta binne gawawwaki a kabarin bai-ɗaya, ta ƙone wasu domin 'ɓoye laifukan yaƙi': Likitocin Sudan
Sojojin Sudan sun harbo jirgi maras matuƙi na RSF a Kordofan ta Arewa
Dakarun Nijar sun cafke muggan makamai da aka yi safararsu daga Libya, sun kama masu safarar ƙwayoyi
RSF ta Sudan ta kai hare-hare a Jihar Khartoum da birnin Atbara bayan amincewa da tsagaita wuta
Paul Biya na Kamaru: Shugaban da ya fi tsufa a duniya ya sha rantsuwar kama aiki karo na takwas
Hatsarin mota ya yi ajalin fiye da mutum 1,000 a Nijar a shekarar 2023, fiye da 12,000 sun jikkata
Sabbin hotunan tauraron dan'adam sun gano alamun 'kaburburan bai-daya a El-Fasher a Sudan
MDD ta yi gargaɗin cewa yaƙin Sudan na gurgunta tattalin arzikin Sudan ta Kudu
Trump ya ce bai kamata Afirka ta Kudu ta kasance cikin G20 ba, ba zai je taronta a Johannesburg ba
'Yan Sudan sun ba da mummunan labarin yi wa mata fyade yayin da suke tserewa daga Al Fasher
An kashe mutane 40 a harin da aka kai wa taron jana'iza a yankin Kordofan na Sudan: MDD