| Hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
An gano wani bam da bai fashe ba a Jihar Neja
Rundunar ‘yansandan Jihar Neja da ke arewa ta tsakiyar Nijeriya ta ce ta gano wani bam da bai fashe ba a ƙauyen Zugurma na ƙaramar hukumar Mashegu.
An gano wani bam da bai fashe ba a Jihar Neja
An gano nakiyar ce bayan wani rahoto da aka samu a ranar Litinin daga Jami'in 'yansanda na Yankin Ibbi da ke Mashegu / Reuters
7 Janairu 2026

Rundunar ‘yansandan Jihar Neja da ke arewa ta tsakiyar Nijeriya ta ce ta gano wani bam da bai fashe ba a ƙauyen Zugurma na ƙaramar hukumar Mashegu.

Jami'in Hulɗa da Jama'a na rundunar, SP Wasiu Abiodun, ya bayyana haka a cikin wata sanarwa a Minna ranar Talata.

Ya ce an gano nakiyar ce bayan wani rahoto da aka samu a ranar Litinin daga Jami'in 'yansanda na Yankin Ibbi da ke Mashegu.

Ya ƙara da cewa wasu mazauna yankin sun ga wani abu da ake zargin bam ne a cikin wani daji da ke yankin.

Abiodun ya ce jami'an 'yansanda na yankin sun yi gaggawar zuwa wurin da lamarin ya faru inda suka killace yankin don tabbatar da tsaron mutane.

Masu AlakaTRT Afrika - ‘Yansandan Nijeriya sun gayyaci Fasto Chris Okafor bisa zarge-zargen aikata fyaɗe

Ya ce Kwamishinan 'Yansandan jihar, Adamu Elleman, ya ba da umarnin tura jami'ai zuwa wajen.

Kakakin 'yansandan ya ce sashen kwance bamabamai na rundunar, wanda CSP Mohammed Mamun ke jagoranta, ya ziyarci wajen a ranar Talata.

Abiodun ya ƙara da cewa jami'an rundunar, tare da al'ummar yankin sun jagoranci tawagar zuwa daidai wurin da aka gano abin.

"Tawagar ta kwance bam ɗin sannan ta miƙa shi ga hedikwatar 'yansandan jihar da ke Minna," in ji shi.

Abiodun ya bayyana cewa an soma gudanar da bincike domin gano inda bam ɗin ya samo asali, yana mai tabbatar da cewa za a fitar da ƙarin sabbin bayanai a kan lamarin nan ba da jimawa ba.

Ya ƙara da cewa Kwamishinan 'yansanda Jihar Neja ya yi kira ga jama'ar yankin su kwantar da hankalinsu, yana mai jaddada cewa dukkan hukumomin tsaro suna nan don tabbatar da tsaro da dawo da zaman lafiya a yankin da kewayensa.

 

Rumbun Labarai
Fiye da mutum 50 ne suka mutu a harin 'yan bindiga a jihar Neja ta tsakiyar Nijeriya
‘Yansandan Nijeriya sun gayyaci Fasto Chris Okafor bisa zarge-zargen aikata fyaɗe
Nijeriya ta kama Indiyawa 22 bisa zargin shigar da hodar ibilis ƙasar
Aƙalla mutane 25 sun mutu, an ceto 13 a hatsarin kwale-kwale a Jihar Yobe ta Nijeriya
An kashe fiye da mutum 30, an sace wasu da dama a Jihar Niger a tsakiyar Nijeriya: 'yansanda
Sojojin Nijeirya sun gano albarusai masu yawa a cikin kwata a Maiduguri
Sakon Shugaba Tinubu na Sabuwar Shekara: Za a tallafa wa mutum 1,000 a kowace mazaɓa a Nijeriya
Abin da bincike ya gano na musabbabin annobar cutar ƙoda a Jihar Yobe
Rundunar sojin Nijeriya ta kashe ‘yan ta’adda 47 a farmaki da ta kai a faɗin ƙasar
Gobara ta ƙona Masallacin Shitta-Bey da ke Lagos wanda ke da alaƙa da Daular Usmaniyya ta Turkiyya
Kotu ta ba da umarnin tsare Abubakar Malami da ɗansa a gidan yarin Kuje
Wani abu ya fashe a Babban Asibiti a Jihar Kebbi ta Nijeriya
‘Yan jarida bakwai sun mutu sakamakon hatsarin mota a Gombe
Siyasar Kano: Shin Kwankwaso ne zai tura Gwamna Abba  Jam'iyyar APC ko kuwa gaban kansa yake son yi?
Shugaba Tinubu ya tafi Turai don ci gaba da hutun ƙarshen shekara
Bam da aka binne a titi ya halaka mutane a Jihar Zamfara, wasu da dama sun jikkata
Mun tuntuɓi Turkiyya domin neman agaji kan matsalar tsaro – Shugaban Nijeriya Tinubu
Hare-haren Amurka sun sauka a wuraren da babu 'yan ƙungiyar Daesh a Sokoto, in ji mazauna yankin
Jirgin Saman Sojin Nijeriya C-130 da aka tsare a Burkina Faso ya isa Portugal domin yin gyara
Da haɗin gwiwarmu Amurka ta kai hari Nijeriya: Ma'aikatar Harkokin Waje