| Hausa
GABAS TA TSAKIYA
2 minti karatu
Ma'aikatar Tsaron Syria ta sanar da tsagaita wuta a wasu unguwannin Aleppo
Ma’aikatar tsaron Syria ta ce ‘yan bindiga suna da zuwa ƙarfe 9 na safe su bar unguwannin da ake rikici da su.
Ma'aikatar Tsaron Syria ta sanar da tsagaita wuta a wasu unguwannin Aleppo
Hukumomin Syria sun sanar da tsagaita wuta a Aleppo bayan aika jami’an tsaro na cikin gida zuwa wuraren da ake rikici / AA
9 Janairu 2026

Ma’aikatar Tsaron Syria ta sanar da tsagaita wuta a wasu unguwanni na arewacin birnin Aleppo, inda ta ce an ɗauki wannan mataki ne domin kawo karshen ayyukan soja a wuraren.

A cewar wata sanarwa da Kamfanin Dillancin Labarai na Syria (SANA) ya wallafa, tsagaita wutar ta fara aiki da misalin karfe 3:00 na asuba agogon cikin gida ranar Juma’a a unguwannin Ashrafieh, Sheikh Maqsoud da Bani Zeid, bayan da hukumomi suka ce an samu cikakken iko a wadannan gundumomi.

Ma’aikatar ta ce an bai wa ƙungiyoyin da ke ɗauke da makamai wa’adin zuwa karfe 9:00 na safiyar ranar Juma’a su fice daga unguwannin, domin a kawo ƙarshen yanayin soja gaba daya.

Wannan sanarwa ta biyo bayan bayanin da Ma’aikatar Cikin Gida ta fitar kan cewa jami’an tsaron cikin gida na Syria sun fara shiga unguwar Ashrafieh, bayan ficewar ƙungiyar ta’addanci ta PKK/YPG daga yankin.

Hukumomi sun ce wannan shigar ta biyo bayan sauya sheƙa da yawancin mambobin YPG suka yi daga Sheikh Maqsoud da Ashrafieh, yayin da wasu kuma suka tsere daga yankunan.

Sojojin Syria sun kuma kai hare-haren bama-bamai masu tsanani a kan wuraren YPG a Aleppo, inda hukumomi suka ce hakan martani ne ga hare-haren da kungiyar ta kai, wadanda suka kashe akalla fararen hula tara tare da jikkata daruruwa.

A ranar 10 ga Maris ɗin 2025, fadar shugaban kasar Syria ta sanar da rattaba hannu kan wata yarjejeniya da nufin shigar da SDF cikin cibiyoyin gwamnati, tare da jaddada hadin kan yankin Syria da kuma kin amincewa da duk wani yunkurin rarrabuwar kasa.

Jami’ai sun ce kungiyar ta’addanci ta YPG ba ta dauki matakai masu ma’ana ba wajen aiwatar da sharuddan yarjejeniyar a watannin da suka biyo baya.

Gwamnati ta kara kaimi wajen kokarin dawo da kuma tabbatar da tsaro a fadin kasar tun bayan kifar da mulkin Bashar al-Assad a ranar 8 ga Disamban 2024, bayan shekaru 24 yana mulki.

 

 

Rumbun Labarai
Iran ba za ta amince da bukatu barkatai ba - Shugaba Pezeshkian
Trump ya yi barazanar ɗaukar 'mataki mai tsanani' kan Iran yayin da Netanyahu ya tafi Washington
Fidan na Turkiyya ya ce amfani da hare-haren sama ba zai rushe gwamnatin Iran ba
Shugaban Iran Pezeshkian ya bayyana tattaunawar nukiliya da Amurka a matsayin 'ci gaba' ga Tehran
Turkiyya da Saudiyya sun jaddada goyon bayansu ga haɗin kan Somaliya da zaman lafiyar yankin
Khamenei ya yi gargaɗi kan yaƙin yanki idan Amurka ta kai hari kan Iran
Iran ta ayyana rundunonin sojin ƙasashen Turai a matsayin 'ƙungiyoyin ta'addanci'
A 'shirye' Iran take don 'yarjejeniyar nukiliya ta gaskiya da adalci': Ministan Harkokin Wajen Iran
Waɗanne abubuwa ne za su iya faruwa idan Amurka ta kai hari Iran?
Iran ta ce duk maƙociyar da ta bari aka yi amfani da ita wurin kai mata hari 'abokiyar gaba' ce
Isra'ila na karya yarjejeniyar tsagaita wuta a Lebanon, ta ci gaba da kai hari
Manyan jami'an China sun tattauna da Ƙungiyar OIC a yanayin da rikicin Gabas ta Tsakiya ke ƙara muni
Yaƙin da ake yi da ta'addancin Daesh yana ƙara ƙarfi: Erdogan
Iran ta gargaɗi Amurka: 'Za mu ɗauki kowane irin hari a matsayin cikakken yaƙi a kanmu'
Turkiyya ba ta goyon bayan tsoma bakin ƙasashe waje a kan Iran – Erdogan
Adadin mutanen da suka mutu a zanga-zangar Iran ya kai  4,000: Rahoto
Syria ta cim ma tsagaita wuta don karɓe iko da arewa maso gabas daga hannun ‘yan ta’addan YPG
Iran ta sha alwashin gwabza yaƙi da duk ƙasar da ta yi gangancin kai wa Khamenei hari
Syria ta ayyana harshen Kurdanci a matsayin 'harshen ƙasa', sannan ta ba Kurdawa haƙƙin 'yan ƙasa
An buɗe sararin samaniyar Iran bayan rufe shi na wucin-gadi