| hausa
AFIRKA
2 minti karatu
WHO ta bayyana damuwa kan karuwar masu ciwon siga a Afirka
Daraktan WHO na yankin Afirka, Dr Mohamed Janabi a wani sako na Ranar Ciwon Siga ta Duniya ya ce nahiyar tana ganin ta’azzarar cutar sikari saboda tsarin yanayin rayuwa mara kyau da karuwar mummunar kiba da teba da kuma rashin tsarin kiwon lafiya mai
WHO ta bayyana damuwa kan karuwar masu ciwon siga a Afirka
WHO ta bayyana damuwa kan karuwar masu fama da ciwon siga a Afirka
11 Nuwamba 2025

Hukumar Lafiya ta Duniya, WHO ta bayyana damuwa kan karuwar masu fama da ciwon siga a fadin Afirka, tana mai kira da a gaggauta yin kokarin magance wannan gagarumar matsala ta lafiya da ke yi wa miliyoyin rayuka barazana.

Daraktan WHO na yankin Afirka, Dr Mohamed Janabi a wani sako na Ranar Ciwon Siga ta Duniya ya ce nahiyar tana ganin ta’azzarar cutar sikari ne saboda tsarin yanayin rayuwa mara kyau da karuwar mummunar kiba da teba da kuma rashin tsarin kiwon lafiya mai kyau.

Ya fayyace cewa akwai mutum fiye da miliyan 24 a Afirka da a yanzu haka suke fama da ciwon siga, wasu alkaluma da ake hasashen za su kai miliyan 60 nan da shekarar 2050, tare da gargadin cewa ba a ma gano rabin masu fama da cutar ba, lamarin da ke jawo mace-macen da za a iya kare afkuwarsu.

Dr Janabi ya ce dole ne gwamnatocin Afirka su karfafa tsarin kiwon lafiyarsu don tabbatar da gano cutar da wuri, da magance ta da kyau da samun kulawa, yana mai cewa idan ba a gano masu dauke da cutar ba, hakan ka iya dakushe tattalin arziki da jawo koma-baya.

Ya fayyace cewa kasashe irin su Ghana da Uganda tuni suka sanya ciwon siga da cututtukan zuciya a cikin tsarin lafiya na matakin farko karkashin shirin WHO Global Diabetes Compact na 2024.

Daraktan WHO na shiyyar Afirkan ya nemi kasashe da zu inganta tsarin lafiya a fannin abinci da motsa jiki da samar da magani a bisa farashi mai rangwame ga kowa, yana mai jaddada cewa gano cutar da wuri da kuma yin sauye-sauye a tsarin rayuwa yana iya rage barazanar kamuwa da cutar sosai.

Rumbun Labarai
Mahaucin Al Fasher: Yadda hotonsa ya zama alamar bakin cikin Sudan
UN Women: Mata da 'yan mata 11M suna fama da matsanancin ƙarancin abinci a Sudan sakamakon yaƙi
Kisan kare dangi a boye da bayyane: Gushewar jinkai a Al Fasher
An ba da belin dan Gaddafi bayan da ya shafe shekaru 10 a tsare a Lebanon
Gwamnatin Trump 'ta aika wa Equatorial Guinea dala miliyan 7.5' don ta karɓi waɗanda Amurka ta kora
Ƙasashe fiye da 20 sun yi Allah wadai da RSF kan kashe-kashen da take yi a Sudan
Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya ya yi kira da a dakatar da zubar da jini a Sudan
Paul Biya na Kamaru: Dan siyasar da zai ci gaba da yin mulki har sai ya kai shekara 99?
Hare-haren RSF sun kori ƙarin dubban mutane daga Darfur da Kordofan na Sudan
RSF ta binne gawawwaki a kabarin bai-ɗaya, ta ƙone wasu domin 'ɓoye laifukan yaƙi': Likitocin Sudan
Sojojin Sudan sun harbo jirgi maras matuƙi na RSF a Kordofan ta Arewa
Dakarun Nijar sun cafke muggan makamai da aka yi safararsu daga Libya, sun kama masu safarar ƙwayoyi
RSF ta Sudan ta kai hare-hare a Jihar Khartoum da birnin Atbara bayan amincewa da tsagaita wuta
Paul Biya na Kamaru: Shugaban da ya fi tsufa a duniya ya sha rantsuwar kama aiki karo na takwas
Hatsarin mota ya yi ajalin fiye da mutum 1,000 a Nijar a shekarar 2023, fiye da 12,000 sun jikkata
Sabbin hotunan tauraron dan'adam sun gano alamun 'kaburburan bai-daya a El-Fasher a Sudan
MDD ta yi gargaɗin cewa yaƙin Sudan na gurgunta tattalin arzikin Sudan ta Kudu
Trump ya ce bai kamata Afirka ta Kudu ta kasance cikin G20 ba, ba zai je taronta a Johannesburg ba
'Yan Sudan sun ba da mummunan labarin yi wa mata fyade yayin da suke tserewa daga Al Fasher
An kashe mutane 40 a harin da aka kai wa taron jana'iza a yankin Kordofan na Sudan: MDD