| Hausa
DUNIYA
2 minti karatu
Fiye da mutum 3,000 ne suka mutu a tafiya ci-rani Turai ta Spain a 2025: Rahoto
Waɗanda suka mutu sun fito ne daga ƙasashe 30, kuma mafi yawansu daga Afirka ta Yamma da Arewacin Afirka, da Pakistan, Siriya, Yaman, Sudan, Iraƙi da Masar.
Fiye da mutum 3,000 ne suka mutu a tafiya ci-rani Turai ta Spain a 2025: Rahoto
Fiye da mutum 3,000 ne suka mutu a tafiya zuwa Spain a 2025: Rahoto / Reuters
31 Disamba 2025

Fiye da mutum 3,000 ne suka mutu a ƙoƙarinsu na kaiwa Spain ta teku a shekarar 2025, in ji wani sabon rahoto, abin da ke nuna babbar raguwa ta yawan mutanen idan aka kwatanta da watanni 12 na baya.

Kungiyar sa-kai ta NGO Caminando Fronteras ta ce mutum 3,090 sun nutse tsakanin Janairu da 15 ga Disamban 2025, ciki har da mata 192 da yara 437.

Wadanda suka mutun sun fito ne daga ƙasashe 30, kuma mafi yawansu daga Afirka ta Yamma da Arewacin Afirka, da Pakistan, Siriya, Yaman, Sudan, Iraƙi da Masar.

Masu fafutuka sun yi gargaɗi cewa raguwar mutuwar ba ta nufin tafiye-tafiyen sun zama masu aminci; maimakon haka suna cewa tsauraran matakan kan iyaka sun tilasta wa 'yan cirani shiga hanyoyi masu ƙarin haɗari.

Rahoton ya gano cewa tsallaken Atlantika daga Arewacin Afirka zuwa Tsibiran Canary ya ci gaba da zama hanyar da ta fi haddasa asarar rai, inda aka samu mutuwar mutane 1,906 a wannan shekara. Tafiyar na iya ɗaukar har zuwa kwanaki 12 a teku.

An ga ƙaruwar 'yan gudun hijira marasa izini sun yi ƙoƙarin bin hanyar daga Aljeriya zuwa Tsibiran Balearic, inda mutane 1,037 suka rasa rayukansu.

Caminando Fronteras ta jaddada bayyanar sabon hanya daga Guinea zuwa Tsibiran Canary, tana nuna ƙaruwa a haɗarurrukan da mutane ke fuskanta yayin ƙoƙarin kaiwa Spain ta teku.

Rahoton ya kuma soki abin da ya kira tsauraran manufofin hijira a duniya a shekarar 2025, tare da mayar da hankali musamman kan Amurka.

A cewar rahoton, manufofin korar ‘yan cirani da Amurka ke jagoranta sun taimaka wajen ƙirƙirar wani tsarin da ke mayar da korar zuwa ƙasashe marasa ƙarfin tattalin arziki, a wasu lokuta wanda ya sa masu ƙaura suke zaune a kurkuku, cikin wani halin rashin tabbas na shari'a, ko ma a sansanonin sojojin Amurka a ƙasashen waje.

Kungiyar ta ce irin waɗannan ayyuka suna koyi da manufofi da aka ɗauka a wasu wurare, ta ambaci shirin Birtaniya na korar masu neman mafaka zuwa Rwanda — wanda daga bisani Kotun Koli ta Birtaniya ta dakatar — da kuma yadda Italiya ta samar da cibiyoyin tsare mutane a Albania.

Rumbun Labarai
WHO: Amurka ta fita daga Hukumar Lafiya ta Duniya bayan shekara 78
Masana kimiyya sun gano zanen shacin hannu 'mai shekara 67,800' a wani kogo a Indonesia
Ministan Wajen Saudiyya da takwarorinsa na Iran, Oman da Qatar sun tattauna kan zaman lafiyar yanki
Amurka ta dakatar da ba da bizar masu ƙaura ga 'yan Nijeriya da wasu ƙasashe 74
Wani sanatan Amurka ya yi gargaɗi kan ƙaruwar ƙyamar Musulunci da ƙin jinin Larabawa
Trump ya saka harajin kashi 25 kan ƙasashen da ke kasuwanci da Iran
An katse intanet da wayoyin hannu a Iran
Matar shugaban Turkiyya ta gana da shugaban UNRWA kan shirin buɗe ofis a Ankara
Sanatocin Republican 5 sun bi sahun 'yan Democrat don neman sake duba ikon yaki na Trump a Venezuela
An kashe ɗansanda a kusa da Tehran yayin da zanga-zanga kan matsin rayuwa ta mamaye ƙasar Iran
Erdogan da Anwar na son ƙarfafa alaƙar Turkiyya da Malaysia tare da fifita fannin tsaro
Trump ya sanya hannu kan takardar neman cire Amurka daga ƙungiyoyin ƙasa da ƙasa da na MDD
Shugaban Rundunar Sojin Iran ya yi barazanar mayar da martani ga Trump da Netanyahu
Abin da ya sa ya kamata Afirka ta damu kan samamen da Amurka ta kai Venezuela
An sayar da kifi mai nauyin kilogiram 240 a kan Naira biliyan 4.5 ($3.2m) a Japan
Me zai faru ga takunkuman da Amurka ta sanya wa Venezuela bayan ta ɗauke Maduro
Tarayyar Afirka ta nuna 'damuwa', Afirka ta Kudu ta nemi a yi taron MDD da gaggawa kan Venezuela
Trump ya gargaɗi Colombia, ya nufi Cuba bayan ya kama Maduro
Amurka ba za ta bari kowa ya ci gaba daga inda Maduro ya tsaya ba - Trump
Martanin duniya na karuwa kan hare-haren da Amurka ta kai wa Venezuela