| Hausa
DUNIYA
3 minti karatu
Tarayyar Afirka ta nuna 'damuwa', Afirka ta Kudu ta nemi a yi taron MDD da gaggawa kan Venezuela
Majalisar Dinkin Afirka da Afirka ta Kudu sun ce, hare-haren Amurka a kan Venezuela sun raina dokokin duniya.
Tarayyar Afirka ta nuna 'damuwa', Afirka ta Kudu ta nemi a yi taron MDD da gaggawa kan Venezuela
The African Union says Venezuelan problem should be addressed through dialogue. / Reuters
4 Janairu 2026

Kungiyar Tarayyar Afirka ta bayyana matuƙar damuwa bayan harin soji na Amurka kan Venezuela da kuma kama Shugaba Nicolás Maduro da gwamnatin Trump ta yi.

"Kungiyar Tarayyar Afirka tana sake tabbatar da dagewarta kan muhimman ƙa'idodin doka na ƙasa da ƙasa, ciki har da girmama ikon ƙasashe, tsaron iyakokinsu, da hakkin al'ummomi na yanke hukunci a kansu, kamar yadda aka shimfida a Yarjejeniyar Majalisar Dinkin Duniya," in ji ƙungiyar ta Afirka a cikin wata sanarwa a ranar Asabar.

Wani jirgin sama da ke ɗauke da Shugaba Maduro ya sauka a New York bayan wani aikin soji na cikin dare na Amurka a Caracas. An fitar da Maduro da matarsa, Cilia Flores, daga jirgin lokacin da suka isa New York, inda aka tuhume su da laifukan miyagun ƙwayoyi da na ta'addanci, waɗanda suka dade suna musantawa.

Bidiyo da wasu kafafen watsa labarai na Amurka suka nuna sun nuna Maduro zagaye da jami'an tsaro yayin da ake yi masa rakiya daga jirgin a Sansanin Jiragen Sama da soji na Stewart.

'Kiyaye kada abin ya ƙara ta'azzara'

Harin Amurka kan ƙasar mai arzikin mai ya janyo fushin duniya kuma ya sa shakku game da tsarin duniya na yanzu.

Kungiyar ta Tarayyar Afirka ta ce 'ta jaddada muhimmancin tattaunawa, sulhu na lumana wajen warware rikice-rikice, da girmama tsarin mulki da na hukumomi, cikin ruhin kyakkyawar maƙwabtaka, haɗin kai, da zaman lafiya tsakanin ƙasashe.'

Kungiyar ta ƙara jaddada cewa za a iya magance matsalolin cikin gida masu rikitarwa da Venezuela ke fuskanta ta hanya mai ɗore ne kawai ta hanyar 'tattaunawa ta siyasa mai faɗi tsakanin 'yan Venezuela da kansu.'

Ta bayyana goyon baya ga mutanen Venezuela kuma ta yi kira ga 'dukkan bangarorin da abin ya shafa su nuna natsuwa, ɗaukar nauyi, da girmama dokokin ƙasa da ƙasa domin hana ƙara ta'azzarar lamarin da kuma kiyaye zaman lafiya da kwanciyar yankin.'

Haka kuma, Afirka ta Kudu a ranar Asabar ta yi kira ga Kwamitin Tsaro na Majalisar Dinkin Duniya da ya yi taro na gaggawa don duba harin sojin Amurka kan Venezuela da kuma kama Shugaba Nicolás Maduro da matarsa.

'Mamayar ƙasashe masu cin gashin kansu'

'Amfani da ƙarfin ba bisa doka ba, na kashin irin wannan yana raunana zaman lafiyar tsarin duniya da kuma ƙa'idar daidaito tsakanin ƙasashe,' in ji Ma'aikatar Harkokin Waje ta Afirka ta Kudu a cikin wata sanarwa a ranar Asabar.

Pretoria ta ƙara da cewa tana lura da matuƙar damuwa game da abubuwan da suka faru a Venezuela kwanan nan kuma tana kallon matakan Amurka a matsayin saɓa Yarjejeniya Kafa Majalisar Dinkin Duniya, wanda ke wajabta wa dukkan ƙasashe membobi su guji barazana ko amfani da ƙarfin da zai shafi tsaron iyakoki ko 'yancin siyasa na kowace ƙasa.

Ta ce kundin bai ba da izinin shiga da sojoji daga waje a cikin al'amuran wata ƙasa ba kan batutuwan da suke hurumin cikin gida na wata ƙasa mai cin gashin kanta ba.

'Tarihi ya nuna cewa mamayewar soja kan ƙasashe masu cin gashin kansu ba ya haifar da komai illa rashin tabbas da zurfafa rikici,' in ji sanarwar.

Masu AlakaTRT Afrika - Trump ya gargaɗi Colombia, ya nufi Cuba bayan ya kama Maduro
Rumbun Labarai
Trump ya gargaɗi Colombia, ya nufi Cuba bayan ya kama Maduro
Amurka ba za ta bari kowa ya ci gaba daga inda Maduro ya tsaya ba - Trump
Martanin duniya na karuwa kan hare-haren da Amurka ta kai wa Venezuela
An fitar da Shugaba Maduro da matarsa daga Venezuela, in ji Trump
Ƙarar bamabamai ta rikita birnin Caracas bayan Trump ya sha alwashin kai hari a ƙasar Venezuela
Zanga-zangar Iran kan matsin tattalin arziki ta rikiɗe zuwa tashin hankali
Hotuna: Wasan tartsatsin wuta da sauran bukukuwa na maraba da Sabuwar Shekara ta 2026
Fiye da mutum 3,000 ne suka mutu a tafiya ci-rani Turai ta Spain a 2025: Rahoto
Somalia ta yi watsi da amincewar da Isra'ila ta yi wa Somaliland a matsayin barazana ga yankin
Turkiyya ta yi tir da Israila kan amincewa da Somaliland
Kiristoci Falasɗinawa sun gudanar da bukukuwan Kirsimeti a Gaza da Gaɓar Yamma
Rasha na shirin gina tashar nukiliya a duniyar wata nan da shekaru 10 masu zuwa
Babban hafsan sojin Libya da jami'ai sun mutu a hatsarin jirgin sama a kusa da Ankara: Dbeibah
Trump ya saka ƙasashen Afirka biyar cikin jerin da ya haramta wa shiga Amurka
Garin da yake shafe kwana 66 a cikin dare babu hasken rana
An kashe sojojin Bangladesh da ke aikin wanzar da zaman lafiya a sansanin MDD na Sudan: Bangladesh
China ta zartar da hukuncin kisa kan tsohon ma'aikacin banki kan karɓar cin hancin dala miliyan 156
Venezuela ta rantsar sabbin sojoji 5,600 yayin da rikici tsakaninta da Amurka ke ƙara tsami
Kundin Guinness World ya dakatar da karbar duk wata buƙata daga Isra’ila: Rahoto
Hotuna: Dubban mutane sun yi maci a Turai da Amurka don nuna wa Falasdinawa goyon baya