| Hausa
AFIRKA
2 minti karatu
Somaliya ta rage lokutan aiki a ofisoshin gwamnati saboda azumin watan Ramadan
A ‘yan shekarun nan tsarin aikin ma'aikata na Somaliya ya kasance abin muhawarar jama'a, musamman game da yawan kwanaki da sa'o'in aiki.
Somaliya ta rage lokutan aiki a ofisoshin gwamnati saboda azumin watan Ramadan
Bisa ga jadawalin watan Ramadan da aka yi wa kwaskwarima, ana sa ran ma'aikatan gwamnati za su yi aiki na kimanin awanni 30 a kowane mako a Somaliya. / Reuters
10 awanni baya

Ma'aikatar Kwadago da Harkokin Jama'a ta Somaliya ta sanar da rage lokutan aiki a hukumance a lokacin watan Ramadan mai alfarma, hakan na bisa ga tsarin ayyukan kwadago da aka daɗe ana yi a ƙasar wadda ke da mafi yawan al’ummar Musulmai.

A cikin wata sanarwa da ta fitar bayan watan ya kankama, ma'aikatar ta isar da gaisuwa ga ma'aikatan Somaliya da kuma al'ummar Musulmi baki ɗaya, tana mai sauyi da aka samu ya nuna muhimmancin watan Ramadan da kuma buƙatar sassautawa ma'aikata masu yin azumi.

A ƙarƙashin tsarin da aka yi wa kwaskwarima, ofisoshin gwamnati za su yi aiki daga ƙarfe 9:00 na safe zuwa 3:00 na yamma, inda aka sanya awanni shida a ranakun aiki ga ma'aikatan gwamnati.

Matakin na da nufin rage yawan aiki da ake gudanarwa yayin da za a ci gaba da muhimman ayyukan gwamnati.

Kodayake, ana sa ran kamfanoni masu zaman kansu za su ci gaba da gudanar da ayyukansu a lokutan da aka saba, amma akwai yiwuwar wasu ‘yan kasuwa suma su iya samar da wani tsari na lokaci mai sauƙi.

Za a rufe wuraren cin abinci

A lokacin Ramadan, gidajen cin abinci da yawa suna rufewa da rana, inda wasu ke rufewa na tsawon watan baki ɗaya, wasu kuma da daddare kawai suke buɗewa don samar da abinci buɗe baki na azumi.

A 'yan shekarun tsarin aikin ma’aikata na Somliya ya kasance batun muhawarar jama'a, musamman game da yawan kwanaki da sa'o'in aiki.

An ware Juma'a a matsayin ranar hutu a cikin mako a hukumance , yayin da ma'aikata da dama ke aiki a ranakun Asabar da Lahadi.

Bisa ga jadawalin watan Ramadan da aka yi wa kwaskwarima, ana sa ran ma'aikatan gwamnati za su yi aiki na kimanin awanni 30 a mako, ko da yake ya danganta da tsarin hutu ko wacce ma’aikata.

Wannan tsarin da aka gabatar ba zai yi aiki a lokaci ɗaya a dukkan fannoni na ma’aikatun ƙasar ba.

Jami'an Sojojin Ƙasa na Somaliya, waɗanda ke ci gaba da fafatawa da Al-Shabaab, da kuma ma'aikatan lafiya a cibiyoyin kiwon lafiya na gwamnati da na masu zaman kansu, za su iya ci gaba ko kuma tsawaita lokaci bisa ga yanayin tsarin aiki da ke sauyawa saboda buƙatu.

Rumbun Labarai
Ma'aikatar mai ta Nijar ta ƙaddamar da dabarun inganta fannin fetur
Turkiyya za ta samar da 'ƙwararan' shirye-shiryen makamashin lantarki da Ethiopia
An bar fasinjoji cirko-cirko a rana ta biyu ta yajin aikin ma'aikatan filin jirgin saman Kenya
Shugaba Erdogan zai kai ziyarar aiki Ethiopia a karon farko cikin fiye da shekaru 10
Harin RSF na watan Oktoban 2025 a Al-Fasher na Sudan ya kashe aƙalla mutum 6,000: Rahoton MDD
AU: Shugabannin Afirka sun ƙaddamar da taron Ƙungiyar Tarayyar Afirka da batun ruwa da sauyin yanayi
Afirka ce kan-gaba wajen faɗaɗa samar da lantarki ta hasken rana a shekarar 2025: Rahoto
Gwamnatin Ghana ta ba da umarnin sarrafa kashi 50 cikin 100 na koko a cikin ƙasar
Sudan: Aƙalla mutum 21 sun mutu a hatsarin kwale-kwale a Kogin Nilu
Kasashe shida sun shiga Kwamitin Tsaro na Tarayyar Afirka
RSF ta kashe ƙananan yara a harin da ta kai wani masallaci a yankin Kordofan na Sudan
Saudiyya ta yi tur da RSF kan munanan ayyukanta a Al Fasher, ta buƙaci a ba da hanyar kai agaji
Mutum biyar sun mutu a hatsarin helikwaftan ɗaukar marasa lafiya a Libya
Yadda 'yan Somaliya suka gina wa tsohon shugaba ƙasarsu Farmaajo sabon gida
Sake dawo da ainihin martabar Afirka
RSF ta Sudan ta kai hari da jirgi maras matuƙi, ta kashe gomman mutane da yara
Dubban ‘yan kasar Libya sun taru don halartar jana'izar Saif al-Islam Gaddafi
Harin RSF a wani asibiti a Sudan ya kashe mutum 22, ciki har da ma'aikatan jinya
Ghana da Zambia sun ƙulla yarjejeniyar shiga ƙasashen juna ba tare da biza ba yayin ziyarar Mahama
Saif al-Islam Gaddafi: An kashe ɗan marigayi shugaban Libya Muammar Gaddafi