| hausa
AFIRKA
2 minti karatu
UN Women: Mata da 'yan mata 11M suna fama da matsanancin ƙarancin abinci a Sudan sakamakon yaƙi
Kimanin kashi 73.7 na mata "ba su da isasshen abinci mai gina jiki, abin da ke nuna matsanancin halin da suke ciki kuma yana ta'azzara yiwuwar fama da tamowa," in ji shirin UN Women.
UN Women: Mata da 'yan mata 11M suna fama da matsanancin ƙarancin abinci a Sudan sakamakon yaƙi
Mutanen da aka raba da gidajensu a Al Fasher suna cikin waɗanda ke fuskantar uƙuba
12 Nuwamba 2025

Shirin da ke kula da harkokin mata na Majalisar Ɗinkin Duniya, UN Women, ya yi kira a ɗauki matakin gaggawa domin kare mata da ‘yan mata a Sudan, inda yaƙin da ake yi yake ta’azzara baƙar yunwar da ta shafi miliyoyin mutane.

"An kwashe fiye da shekaru biyu a fagen daga a Sudan lamarin da ya kassara rayuwar mata da ‘yan mata da raba su da gidajensu da makomarsu, inda suke ɗanɗana kuɗarsu sakamakon wannan babban bala’i na rikicin Sudan," a cewar Anna Mutavati, daraktar Gabashi da Kudancin Afirka ta Shirin UN Women, a hira da manema labara a Geneva ranar Talata.

Alƙaluman da UN Women ya fitar game da yanayin samun abinci da rashin tsaro a Sudan sun nuna cewa mata da ‘yan mata kimanin miliyan 11 na fama da matsanancin ƙarancin abinci.

"Kasancewa mace a Sudan wata babbar alama ce ta fuskantar yunwa," in ji Mutavati.

Ta ƙara da cewa a yayin da yaƙi yake ƙamari a Al Fasher sannan ake ci gaba da fama da ƙarancin abinci a faɗin Darfur, mata da ‘yan mata suna fuskantar "matsananciyar yunwa da kora daga gidajensu da kisa da lalata da musgunawa."

Lamarin ya ta’azzara ne bayan a hukumance an ayyana yankin Al Fasher da Kadugli a matsayin wuraren da ke fama da matsananciyar yunwa a watan Nuwamba.

MDD ta yi kira a yi gaggawar taimaka wa mata

Bayanan da shirin UN Women ya fitar sun nuna cewa Kimanin kashi 73.7 na mata "ba su da isasshen abinci mai gina jiki, abin da ke nuna matsanancin halin da suke ciki kuma yana ta'azzara yiwuwar fama da tamowa."

Mutavati ta jaddada buƙatar gaggawa ta tabbatar da ganin an bai wa mata da ‘yan mata agajin jinƙai da suka shafi buƙatunsu, tana mai cewa su ne suka fi galabaita a yaƙin Sudan.

Rumbun Labarai
Mahaucin Al Fasher: Yadda hotonsa ya zama alamar bakin cikin Sudan
WHO ta bayyana damuwa kan karuwar masu ciwon siga a Afirka
Kisan kare dangi a boye da bayyane: Gushewar jinkai a Al Fasher
An ba da belin dan Gaddafi bayan da ya shafe shekaru 10 a tsare a Lebanon
Gwamnatin Trump 'ta aika wa Equatorial Guinea dala miliyan 7.5' don ta karɓi waɗanda Amurka ta kora
Ƙasashe fiye da 20 sun yi Allah wadai da RSF kan kashe-kashen da take yi a Sudan
Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya ya yi kira da a dakatar da zubar da jini a Sudan
Paul Biya na Kamaru: Dan siyasar da zai ci gaba da yin mulki har sai ya kai shekara 99?
Hare-haren RSF sun kori ƙarin dubban mutane daga Darfur da Kordofan na Sudan
RSF ta binne gawawwaki a kabarin bai-ɗaya, ta ƙone wasu domin 'ɓoye laifukan yaƙi': Likitocin Sudan
Sojojin Sudan sun harbo jirgi maras matuƙi na RSF a Kordofan ta Arewa
Dakarun Nijar sun cafke muggan makamai da aka yi safararsu daga Libya, sun kama masu safarar ƙwayoyi
RSF ta Sudan ta kai hare-hare a Jihar Khartoum da birnin Atbara bayan amincewa da tsagaita wuta
Paul Biya na Kamaru: Shugaban da ya fi tsufa a duniya ya sha rantsuwar kama aiki karo na takwas
Hatsarin mota ya yi ajalin fiye da mutum 1,000 a Nijar a shekarar 2023, fiye da 12,000 sun jikkata
Sabbin hotunan tauraron dan'adam sun gano alamun 'kaburburan bai-daya a El-Fasher a Sudan
MDD ta yi gargaɗin cewa yaƙin Sudan na gurgunta tattalin arzikin Sudan ta Kudu
Trump ya ce bai kamata Afirka ta Kudu ta kasance cikin G20 ba, ba zai je taronta a Johannesburg ba
'Yan Sudan sun ba da mummunan labarin yi wa mata fyade yayin da suke tserewa daga Al Fasher
An kashe mutane 40 a harin da aka kai wa taron jana'iza a yankin Kordofan na Sudan: MDD