| Hausa
DUNIYA
2 minti karatu
Amurka ba za ta bari kowa ya ci gaba daga inda Maduro ya tsaya ba - Trump
A yanzu Amurka za ta yanke shawara kan makomar Venezuela bayan "kama" Maduro", a cewar Shugaba Trump, yana mai ƙarawa da cewa "za mu shiga cikin samar da sabon shugaba sosai."
Amurka ba za ta bari kowa ya ci gaba daga inda Maduro ya tsaya ba - Trump
A destroyed anti-aircraft unit is seen at La Carlota military air base in Venezuela after US strikes. / Reuters
3 Janairu 2026

Amurka yanzu tana yanke shawara kan abin da zai biyo baya ga Venezuela bayan "kama" Shugaban ƙasa Nicolas Maduro da matarsa Cilia Adela Flores, in ji Shugaban Amurka Donald Trump, yana mai ƙarawa da cewa Washington "za ta shiga cikin sa sosai".

"Za mu shiga cikin sa sosai. Kuma muna son samar da 'yanci ga mutane," kamar yadda Trump ya gaya wa Fox News a wata hira ta waya ranar Asabar, yana mai ƙarawa da cewa wannan gagarumin hari na rundunar soji na musamman na Amurka ya nuna cewa "ba za a rinjayi washington ba."

Trump ya ƙara da cewa Amurka za ta sa “hannu dumu-dumu” a ɓangaren man fetur ɗin Venezuela.

"Muna da kamfanonin mai mafiya ƙarfi a duniya, mafiya girma, mafiya kyau, kuma za mu shiga sosai cikin harkar," in ji shi.

Masu AlakaTRT Afrika - Tarayyar Afirka ta nuna 'damuwa', Afirka ta Kudu ta nemi a yi taron MDD da gaggawa kan Venezuela

Trump ya ce Maduro da matarsa suna wani jirgin ruwa na yaƙi na Amurka kuma za su fuskanci gurfanarwa a New York.

Ya ce an kama Maduro a wani wuri da ake gadinsa sosai, kuma ya ƙara da cewa babu Amurkawa da aka kashe a harin na soji na ranar Asabar.

"Yana cikin wani wuri da ake gadinsa sosai," in ji Trump. "Ku sani, abin mamaki ne cewa babu wanda muka rasa," kamar yadda ya faɗa, yana ƙarawa da cewa "wasu sun ɗan ji rauni, amma sun dawo kuma ana sa ran za su kasance cikin koshin lafiya."

"Na kalli komai, da gaske, kamar ina kallon shirin talabijin," kamar yadda Trump ya bayyana.

"Mun kalli kowane ɓangare na aikin."

Rumbun Labarai
WHO: Amurka ta fita daga Hukumar Lafiya ta Duniya bayan shekara 78
Masana kimiyya sun gano zanen shacin hannu 'mai shekara 67,800' a wani kogo a Indonesia
Ministan Wajen Saudiyya da takwarorinsa na Iran, Oman da Qatar sun tattauna kan zaman lafiyar yanki
Amurka ta dakatar da ba da bizar masu ƙaura ga 'yan Nijeriya da wasu ƙasashe 74
Wani sanatan Amurka ya yi gargaɗi kan ƙaruwar ƙyamar Musulunci da ƙin jinin Larabawa
Trump ya saka harajin kashi 25 kan ƙasashen da ke kasuwanci da Iran
An katse intanet da wayoyin hannu a Iran
Matar shugaban Turkiyya ta gana da shugaban UNRWA kan shirin buɗe ofis a Ankara
Sanatocin Republican 5 sun bi sahun 'yan Democrat don neman sake duba ikon yaki na Trump a Venezuela
An kashe ɗansanda a kusa da Tehran yayin da zanga-zanga kan matsin rayuwa ta mamaye ƙasar Iran
Erdogan da Anwar na son ƙarfafa alaƙar Turkiyya da Malaysia tare da fifita fannin tsaro
Trump ya sanya hannu kan takardar neman cire Amurka daga ƙungiyoyin ƙasa da ƙasa da na MDD
Shugaban Rundunar Sojin Iran ya yi barazanar mayar da martani ga Trump da Netanyahu
Abin da ya sa ya kamata Afirka ta damu kan samamen da Amurka ta kai Venezuela
An sayar da kifi mai nauyin kilogiram 240 a kan Naira biliyan 4.5 ($3.2m) a Japan
Me zai faru ga takunkuman da Amurka ta sanya wa Venezuela bayan ta ɗauke Maduro
Tarayyar Afirka ta nuna 'damuwa', Afirka ta Kudu ta nemi a yi taron MDD da gaggawa kan Venezuela
Trump ya gargaɗi Colombia, ya nufi Cuba bayan ya kama Maduro
Martanin duniya na karuwa kan hare-haren da Amurka ta kai wa Venezuela
An fitar da Shugaba Maduro da matarsa daga Venezuela, in ji Trump