Yaya karawar Nijeriya da Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo za ta kasance?
NIJERIYA
4 minti karatu
Yaya karawar Nijeriya da Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo za ta kasance?Ƙasashen biyu dai sau shida ne suka taɓa haduwa a tarihin ƙwallon ƙafa.
Nijeriya ta doke Gabon da 4-1 kafin ta kai wannan matakin
14 Nuwamba 2025

A ranar Lahadi ne tawagar ƙwallon ƙafar Nijeriya, Super Eagles za ta kara da takwararta ta Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo a wasan neman shiga Gasar Cin Kofin Duniya ta 2020.

Kafin su kai ga wannan matsayin ƙasashen biyu sun samu nasara a wasannin da suke buga ranar Alhamis.

Nijeriya ta doke Gabon ne da 4-1, yayin da Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo ta doke Kamaru da 1-0.

Sai dai kuma tawaga ɗaya ce za ta wakilci nahiyar Afirka a ƙoƙarin neman cike gurbi ɗaya da ya saura da nahiyar za ta iya cikewa a Gasar Cin Kofin Duniya ta shekarar 2026.

Duk tawagar da ta yi nasara za ta wakilci Afirka a wasannin cike gurbin shiga Gasar Cin Kofin Duniya da za a yi a watan Maris na shekarar 2026.

Tarihin karawar ƙasashen biyu

Bari mu dubi tarahin karawar ƙasashen biyu a fagen tamaula da kuma tarihin ƙasashen biyu a Gasar Cin Kofin Duniya.

Ƙasashen biyu dai sau shida ne suka taɓa haduwa a tarihin ƙwallon ƙafa.

Nijeriya ta doke Kongo sau biyu inda Kongo ta doke Nijeriya sau uku, kuma ƙasashen suka tashi canjaras sau ɗaya.

Ranar 5 ga watan Nuwamban shekarar 1966 ne Nijeriya ta fara karawa da Kongo inda ta doke ta da 3-2.

Sai dai kuma Kongo ta ɗau fansa ranar 26 ga watan Nuwamban shekarar 1966 inda ta doke Nijeriya da ci ɗaya mai ban haushi.

Ƙasashen sun sake karawa ranar 27 ga watan Disamban shekarar 1966 inda Kongo ta sake doke Nijeriya da ci ɗaya da nema.

Tawagogin biyu ba su sake haɗuwa ba sai lokacin da suka kara ranar uku ga watan Maris na shekarar 2010 inda Nijeriya ta lallasa Kongo da ci 5-2.

Sai kuma shekarar 2015 inda Kongo ta doke Nijeriya da biyu da nema.

Karawar ƙarshe ita ce haɗuwarsu a ranar 28 ga watan Mayu inda suka tashi kunnen doki.

Muhimman ‘yan wasa

Duk da cewa ƙasashen biyu suna cike da ƙwararrun ‘yan wasan, akwai wasu ‘yan wasan da ake sa ran za su taka rawar gani a wasan da za a buga ranar Lahadi.

Victor Osimhen: Ɗan wasan gaban Galatasaray ta Turkiyya na kan ganiyarsa inda yake taimaka wa ƙasarsa Nijeriya da ƙungiyar da yake bugawa zura ƙwallaye a raga.

Ya zura ƙwallaye har biyar a raga a wasanni biyu na baya bayan nan da ya buga wa Nijeriya.

Aaron Wan-Bissaka da ke murza leda a ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta West Ham ya fara taka wa Kongo leda ne a watan Satumban shekarar 2025 inda ya ƙarfafa bayan tawagar ta Kongo.

Chancel Mbemba shi ne ya ci ƙwallo ɗaya tilon da ya bai wa Kongo damar nasara kan Kamaru fiye da minti 90 da fara wasa.

Mbemba dai yana taka leda a ƙungiyar Lille ta ƙasar Faransa kuma yana cikin waɗanda za a mayar da hankali a kansu a wasan da ƙasarsa za ta yi da Nijeriya a ranar Lahadi.

Benjamin Fredric ɗan wasa bayan ne da yake buga wasan aro a ƙungiyar Dender EH ta Belgium ɗan wasan ne mai shekara 20. Yana cikin ‘yan wasan da Nijeriya ke ji da shi da shi.

Ɗan wasan na baya bangaren dama ya taka rawa a nasarar da Nijeriya ta yi a kan Gabon inda ya hana ‘yan wasan Gabon irin su Aubermeyang sakat.

Arthur Masuaku da ke wasa a Sunderland na cikin ‘yan wasan da suka fi ƙwarewa a tawagar Kongo. Ɗan wasan na baya ya yi suna wajen iya kai hari daga baya.

Akor Adams: Ɗan wasan gaban Nijeriya ne da ke taka leda a ƙungiyar Sevilla ta Sifaniya. Shi ya fara zura ƙwallo a ragar Gabon a karawarta da Nijeriya. Yana cikin ‘yan wasan da manazarta za su fi mayar da hankali a kansu ranar Lahadi.

Axel Tuanzbe: Dan wasa ne da ke taka leda a ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Burnley da ke Ingila. Ya buga wasanni tara cikin 10 da tawagar ta Kongo ta buga a wasannin neman  shiga Gasar Cin Kofin Duniya.

Rumbun Labarai
Jerin lokutan da aka shafe ana shari'ar Nnamdi Kanu, jagoran 'yan a-waren Biafra a Nijeriya
Yadda ta kaya a zaman 'yan majalisar Amurka kan zargin yi wa Kirisotci kisan kiyashi a Nijeriya
‘Yan bindiga sun sace ɗalibai da ma’aikata a wata makaranta a Jihar Neja
Jagoran ƴan-awaren Biafra: Babbar Kotu a Nijeriya ta yanke wa Nnamdi Kanu hukuncin ɗaurin rai da rai
'Yan Nijeriya miliyan 45 suna bahaya har yanzu a waje — Ministan Muhalli
Ribadu ya jagoranci wata tawagar Nijeriya mai ƙarfi zuwa Amurka kan zargin kashe Kiristoci a ƙasar
Kotu ta yanke wa wani shugaban ISWAP da ya tsara hare-haren kano na 2012 ɗaurin shekara 20
Tinubu ya ɗaga tafiyarsa tarukan G20 da AU-EU saboda yanayin rashin tsaro da ake ciki a Nijeriya
Majalisar Dattawan Nijeriya ta nemi a ɗauki ƙarin sojoji 100,000 don magance rashin tsaro
Tinubu ya yi alhinin mutuwar Janar Uba da 'yan ta'adda suka kashe a Borno
Majalisar Dokokin Amurka za ta binciki zargin yi wa Kiristoci kisan kiyashi a Nijeriya ranar Alhamis
Gwamnatin Jihar Katsina za ta shirya muƙabala tsakanin Yahya Masussuka da sauran Malaman Musulunci
Babban hafsan sojin Nijeriya ya je Jihar Kebbi ya nemi  a tsaurara neman 'yan matan da aka sace
Gwamnatin Nijeriya ta umarci jami’an tsaro su kuɓutar da ɗalibai mata da aka sace a Jihar Kebbi
Nijeriya tana tattaunawa kan tsaro da Amurka bayan barazanar Trump: Yusuf Tuggar
Gwamnatin Nijeriya ta ƙaddamar da tallafin jarin N50m ga ɗalibai a fannin ƙirƙire-ƙirƙire
Rikicin PDP: Ɓangaren Wike ya yi watsi da kora yayin da jihohi huɗu ke ƙalubalantar Makinde
‘Yan sandan Nijeriya sun tabbatar da sace ɗalibai ‘yan mata 25 a Kebbi
Sojojin Nijeriya sun daƙile kwanton-ɓauna, sun yi watsi da jita-jitar sace wani janar na soja
Kasafin kuɗin gwamnatin kano na 2026 zai haura naira tiriliyan ɗaya - Gwamna Abba Kabir