| hausa
AFIRKA
2 minti karatu
Rubio ya nemi a daina bai wa RSF makamai, ya ɗora wa rundunar laifi kan kashe-kashe a Al Fasher
Ministocin ƙasashen ƙungiyar G7 sun bayyana goyon bayansu ga yunƙurin diflomasiyya na neman kawo ƙarshen yaƙin Sudan, inda suka yi kira ga masu ruwa da tsaki na ƙasashen waje su goyi bayan yunƙurin.
Rubio ya nemi a daina bai wa RSF makamai, ya ɗora wa rundunar laifi kan kashe-kashe a Al Fasher
Ƙazamin yaƙin tsakanin sojojin Sudan da dakarun RSF, wanda aka soma a Afrilun 2023, ya kashe aƙalla mutum 40,000
9 awanni baya

Sakataren Wajen Amurka Marco Rubio ya yi kira ga masu ruwa da tsaki na ƙasashen duniya su daina bayar da makamai ga mayaƙan rundunar Rapid Support Forces na Sudan, inda ya ɗora musu alhakin ta’azzarar zubar da jini a ƙasar.

"Ina gani ya kamata a yi wani abu domin daina bayar da makamai da goyon baya ga RSF a yayin da suke ci gaba da ƙaimi da mamaye wurare," a cewar Rubio a hira da manema labarai ranar Laraba a yayin da yake barin wurin taron ministocin ƙasashen waje na ƙungiyar ƙasashen (G7) a Canada.

Ministocin ƙasashen waje na ƙungiyar G7 sun yi Allah wadai bisa “hare-haren ƙalibanci” da mayaƙan Rapid Support Forces (RSF) da ke Sudan suke kai wa fararen-hula da ba su da laifi da kuma ma’aikatan agaji a Al Fasher da North Kordofan.

Masu AlakaTRT Afrika - Mahaucin Al Fasher: Yadda hotonsa ya zama alamar bakin cikin Sudan

Wata sanarwar haɗin gwiwa da suka fitar bayan kammala taron na kwanaki biyu a Niagara, Canada, manyan jami’an diflomasiyya daga ƙasashen Canada, Faransa, Jamus, Italiya, Japan, Birtaniya da Amurka — tare da wakilin Hukumar Tarayyar Turai — sun yi kakkausar suka game da "mummunan tasirin da wannan yaƙi yake yi a kan fararen-hula, ciki har da matsananciyar yunwa da ta haddasa larurar rashin jinkai mafi muni a duniya."

"Mun yi Allah wadai da da kakkausar murya kan yadda ake yin lalata da mata. Muna kira ga dakarun Rapid Support Forces (RSF) da na Rundunar Sojin Sudan (SAF) su yi biyayya ga tsarin kare hakkin ɗan’adam, tare da tsagaita wuta nan-take da kuma bari a shigar da kayan agaji ba tare da jinkiri ba," in ji sanarwar da suka fitar ranar Laraba.

Kazalika ministocin sun nuna goyon bayansu ga “yunƙurin diflomasiyya da ake yi na maido da zaman lafiya da tsaro” tare da yin kira ga masu ruwa da tsaki na ƙasashen duniya su bayar da tasu gudunmawar wajen tabbatar da zaman lafiya.

An kashe dubban mutane, an raba miliyoyi da matsugunansu

Hakan na faruwa ne a yayin da MDD ta yi gargaɗi cewa halin da ake ciki a Sudan yana ci gaba da taɓarɓarewa musamman ga fararen-hula, sannan ƙungiyoyin bayar da agaji sun ce suna fuskantar kalubale wajen shiga yankunan da yaƙin ya shafa.

An soma yaƙi tsakanin sojojin Sudan da mayaƙan RSF a watan Afrilun 2023, kuma kawo yanzu ya yi sanadin mutuwar aƙalla mutum 40,000 tare da raba fiye da mutum miliyan 12 da muhallansu, a cewar Hukumar Lafiya ta Duniya.

Rumbun Labarai
UN Women: Mata da 'yan mata 11M suna fama da matsanancin ƙarancin abinci a Sudan sakamakon yaƙi
WHO ta bayyana damuwa kan karuwar masu ciwon siga a Afirka
Kisan kare dangi a boye da bayyane: Gushewar jinkai a Al Fasher
An ba da belin dan Gaddafi bayan da ya shafe shekaru 10 a tsare a Lebanon
Gwamnatin Trump 'ta aika wa Equatorial Guinea dala miliyan 7.5' don ta karɓi waɗanda Amurka ta kora
Ƙasashe fiye da 20 sun yi Allah wadai da RSF kan kashe-kashen da take yi a Sudan
Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya ya yi kira da a dakatar da zubar da jini a Sudan
Paul Biya na Kamaru: Dan siyasar da zai ci gaba da yin mulki har sai ya kai shekara 99?
Hare-haren RSF sun kori ƙarin dubban mutane daga Darfur da Kordofan na Sudan
RSF ta binne gawawwaki a kabarin bai-ɗaya, ta ƙone wasu domin 'ɓoye laifukan yaƙi': Likitocin Sudan
Sojojin Sudan sun harbo jirgi maras matuƙi na RSF a Kordofan ta Arewa
Dakarun Nijar sun cafke muggan makamai da aka yi safararsu daga Libya, sun kama masu safarar ƙwayoyi
RSF ta Sudan ta kai hare-hare a Jihar Khartoum da birnin Atbara bayan amincewa da tsagaita wuta
Paul Biya na Kamaru: Shugaban da ya fi tsufa a duniya ya sha rantsuwar kama aiki karo na takwas
Hatsarin mota ya yi ajalin fiye da mutum 1,000 a Nijar a shekarar 2023, fiye da 12,000 sun jikkata
Sabbin hotunan tauraron dan'adam sun gano alamun 'kaburburan bai-daya a El-Fasher a Sudan
MDD ta yi gargaɗin cewa yaƙin Sudan na gurgunta tattalin arzikin Sudan ta Kudu
Trump ya ce bai kamata Afirka ta Kudu ta kasance cikin G20 ba, ba zai je taronta a Johannesburg ba
'Yan Sudan sun ba da mummunan labarin yi wa mata fyade yayin da suke tserewa daga Al Fasher
An kashe mutane 40 a harin da aka kai wa taron jana'iza a yankin Kordofan na Sudan: MDD