| Hausa
SIYASA
2 minti karatu
Alkawarin dala miliyan 150 zai sake gina Aleppo da yaƙi ya lalata
Taron hada kudade na kwanaki uku karkashin jagorancin Ofishin Gwamnan Aleppo ya smau gagarumin goyon baya a yayin da birni na biyu mafi girma a Syria ke gwagwarmayar farfadowa bayan yakin da aka gwabza na shekaru da hare-haren Isra’ila.
Alkawarin dala miliyan 150 zai sake gina Aleppo da yaƙi ya lalata
Gangamin ya nemi a tara kudade don farfado da yankin Aleppo da yaki da lalata. / AA
19 Disamba 2025

Jami'ai sun ce wani gangamin bayar da gudunmawa da nufin sake gina lardin Aleppo da ya lalace a Syria ya tara dala miliyan 150 a ranar Alhamis, wanda hakan ke nuna babban ci gaba a fannin kudi ga kokarin sake gina daya daga cikin yankunan da suka fi fama da matsala a kasar.

An kaddamar da gangamin na kwanaki uku a karkashin jagorancin Fadar Gwamnan Aleppo, wanda ke neman samar da kudaden da za a mayar da kayayyakin more rayuwa, gidaje, da ayyukan jama'a bayan fiye da shekaru goma na yaki da ya barke a birnin.

Mashirya taron sun ce za a yi amfani da kudaden ne ga ayyukan ci gaba da ake bukata cikin gaggawa don farfado da rayuwar yau da kullum a cibiyar kasuwanci ta tarihi.

Aleppo ya fuskanci wasu daga cikin rikice-rikice mafi zafi a lokacin yakin basasar Syria, inda unguwannin garin suka lalace kuma muhimman ayyuka cibiyoyin ayyuka suka gurgunce.

Duk da kawo karshen fadace-fadace, birnin na ci gaba da fuskantar kalubalen sake gina shi, wanda ya haifar da irin wannan yunkurin na tara kudi a wasu larduna.

Cigaba da kai hare-hare daga Isra’ila

 Wannan gangamin ya zo ne a daidai lokacin da sojojin Isra'ila ke kara kai hare-hare Syria, wanda Damascus ta ce ya kara kawo cikas ga murmurewar kasar.

Bayanan gwamnatin Syria sun nuna cewa tun daga Disamban 2024, Isra'ila ta kai hare-hare ta sama sama da 1,000 a fadin kasar da kuma hare-hare sama da 400 a kan iyakokinta zuwa lardunan kudu, inda ta kashe fararen hula da kuma lalata cibiyoyin soji da kayayyakin more rayuwa.

Bayan faduwar gwamnatin Bashar al-Assad a karshen shekarar 2024, Isra'ila ta kuma fadada mamayar da take yi a Tuddan Golan na Syria ta hanyar kwace wani yanki mai tsaro da ba shi da makami - matakin da Syria ta ce ya saba wa yarjejeniyar janyewa daga yankin ta shekarar 1974.

Jami'ai sun ce ci gaba da tallafa wa kasashen duniya da na cikin gida zai zama muhimmi idan Aleppo za ta sake ginuwa bayan shekaru na yaki da kuma tashin hankali a yankin.

Rumbun Labarai
Yadda 'yan Nijeriya suka fusata kan matakin Amurka na saka wa Kwankwaso takunkumi
Majalisar Dattijan Nijeriya ta amince da tsarin aika sakamakon zabe kai-tsaye ta intanet
Taƙaddama a kan gyaran dokar zaɓe ta Nijeriya
Ghana ta yi wa jakadanta a Nijeriya kiranye kan zargin maguɗin zaɓe
Iran ta ce ta shiga tattaunawar Oman da Amurka da 'kyakkyawar niyya'
Masar da Saudiyya sun yi kira ga samar da hanyoyin da suka dace kafin tattaunawar Amurka da Iran
Greenland ba hajar sayarwa ba ce
Yayin da duniya ta koma kasuwar buƙatar diflomasiyya, wai zai tsaya wa ƙasashe marasa ƙarfi a 2026?
Amurka ta dakatar da bai wa ‘yan Nijeriya biza
Yadda 'nadamar zalunci' ke janyo rushewar lafiyar ƙwaƙwalwa a rundunar sojin Isra’ila
Me ya sa Trump da masu sharhi da ke da ra’ayin rikau ke sa ido kan al’ummar Somalia da ke Minnesota?
Shugaban Nijar Tiani ya karɓi shugaban Bilma bayan ya yi watanni 16 a hannun masu garkuwa da mutane
An daƙile harin RSF kan West Kordofan: Rundunar Sojin Sudan
Nijar ta ce ta fara kai uranium ɗinta kasuwar duniya
Trump ya ce Amurka za ta dakatar da hijirar 'yan cirani daga kasashe marasa arziki har abada
Gobarar Hong Kong: Adadin waɗanda suka mutu ya kai 128 yayin da aka shiga kwana uku a ƙoƙarin ceto
China ta yi gargaɗin 'murƙushe' katsalandan ɗin ƙetare kan shirin makami mai linzani na Japan
Yaƙin Sudan: Maye gurbin UAE da Turkiyya na iya ƙarfafa ƙoƙarin ƙasashe na samar da zaman lafiya
Jam’iyyar PDP ɓangaren Kabiru Turaki ta ɗage zaman kwamitin gudanarwarta na farko saboda hargitsi
Yadda muhawarar Kyamar Musulunci a Birtaniya ta fito da munafurcin kasar