| hausa
WASANNI
2 minti karatu
Za a iya dakatar da Ronaldo buga wasanni biyu bayan ya samun jan kati
Akwai yiwuwar kyaftin din kasar Portugal Cristiano Ronaldo zai fuskanci dakatarwa daga buga wasanni biyu – watakila ciki har da wasan farko da kasarsa za ta buga a Gasar Cin Kofin Duniya na 2026 sakamakon jan katin da ya samu a wasan da kasarsa ta yi
Za a iya dakatar da Ronaldo buga wasanni biyu bayan ya samun jan kati
An bai wa Ronaldo jan kati a karawar Portugal da Ireland
14 Nuwamba 2025

Portugal ta yi rashin nasara ne a hannun Ireland da ci 2-0 kuma wannan ne wasa na farko da shahararren dan wasan ya samu jan kati, bayan ya yi wa kasarsa ta Portugal wasanni 220 a tarihi.

Alkalin wasan ya kori Ronaldo ne bayan ya yi wa dan wasan bayan Ireland Dara O’Shea gula yayin wasan neman zuwa Gasar Cin Kofin Duniya da suka buga a birnin Dublin ranar Alhamis.

Korar dan wasan da aka yi za ta iya jawo masa rasa damarsa ta buga wasan farko da Portugal za ta buga a gasar a shekara mai zuwa, idan kasarsa ta samu damar zuwa gasar.

Da farko alkalin wasan ya fara bai wa shahararren dan wasan katin gargadi ne kafin daga bisani ya duba bidiyon da yake taimaka wa alkalin wasa yanke hukunci, sannan ya ba shi jan kati kai-tsaye.

A karkashin dokokin hukumar FIFA, za a iya dakatar da dan wasa buga wasanni biyu idan ya aikata laifukan rashin da’a irin wanda Ronaldo ya aikata.

Ronaldo ya zargi Kocin Ireland Heimir Hallgrimsson kan cewa shi ne ya matsa wa alkalin wasa lambar har ya sauya matsayarsa daga katin gargadin da ya fara ba shi zuwa jan kati.

Sai dai kocin ya ce kuskure ne dan wasan ya ce shi ne ya ja aka ba shi jan kati, kocin ya ce laifin da ya aikata ne ya jawo masa jan katin kuma ya ce wani karamin kuskure ne da ya yi sila.

Rumbun Labarai
Zuwa Gasar Kofin Duniya ta 2026: Abin da ya jawo rashin nasarar Nijeriya a karawarta da DRC
Kotu a Jamus ta goyi bayan danwasan da aka kora kan goyon bayan Falasdinu
Shugaban Barcelona ya gwale Messi kan yiwuwar komawarsa Barca
Hukumar ƙwallon ƙafar Sifaniya ta maye gurbin Lamine Yamal da Jorge de Frutos
Yves Bissouma: An kwashe wa danwasan Tottenham fam 800,000 daga asusun banki
Kocin Man United ya mayar wa Ronaldo martani kan sukar halin da kungiyar ke ciki
'Agent' ya saka wa dan wasan Tottenham bindiga a ka don ya tursasa shi
Tawagar Portugal za ta saka jesin karrama tsohon ɗan wasanta bakar fata
Mutum 41,000 daga kasashe 126 ne suka shiga wasan tseren sassarfa na Istanbul karo na 47
Yadda kwazon Yamal a filin wasa ya ragu saboda ciwon matsematsi
Da gaske ne Barcelona za ta nemi Victor Osimhen don maye gurbin Robert Lewandowski?
Kotu ta umarci Barcelona ta fito da takardun biyan dala miliyan 9 ga wani rafari
Yamal zai kashe $16m don sayen gidan da Pique da Shakira suka zauna
Mohamed Salah ya cire Liverpool daga shafukansa na sada zumunta bayan wasansu da Frankfurt
Osimhen, Salah, Hakimi: Jerin sunayen ‘yan wasan da ke takarar gwarzon shekara na CAF
‘Yan Nijeriya uku za su taka leda a Gasar Zakarun Turai ranar Laraba
Ronaldo ba zai je India buga wasan Al-Nassr da Goa ba
Alonso ya yaba wa Vinicius kan janyo wa 'yan wasan Getafe biyu samun jan kati
Messi ya jajanta wa tawagar Argentina bayan Morocco ta doke su, ta ɗaga Kofin FIFA U20
Morocco ta ɗauki kofin duniya na ‘yan ƙasa da shekara 20 bayan ta doke Argentina