| hausa
TURKIYYA
2 minti karatu
Shugaban Turkiyya Erdogan ya yi maraba da yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza
Erdogan ya jaddada goyon bayan Turkiyya na kafa ƙasar Falasɗinu mai cin gashin kanta.
Shugaban Turkiyya Erdogan ya yi maraba da yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza
Shugaban Turkiyya Erdogan ya jinjina wa Falasɗinawa bisa jajircewarsu da mutunta kawunansu
9 Oktoba 2025

Shugaban Turkiyya Recep Tayyip Erdogan ya bayyana gamsuwarsa game da yarjejeniyar tsagaita wuta da aka ƙulla tsakanin Isra’ila da ƙungiyar gwagwarmaya ta Hamas ta Falasɗinawa bayan tattaunawar da aka yi a birnin Sharm el-Sheikh na ƙasar Masar, wada Turkiyya ta taka rawa a cikinta.

A sanarwar da ya fitar ranar Alhamis, Erdogan ya gode wa shugaban Amurka Donald Trump bisa nuna dattako na siyasa wajen sanyawa Isra’ila ta saka hannu kan yarjejeniyar, kana ya miƙa godiya ga ƙasashen Qatar da Masar bisa muhimmiyar rawar da suka taka wajen cim ma yarjejeniyar.

Shugaban ƙasar Turkiyya ya ce Turkiyya za ta bibiyi aiwatar da yarjejeniyar tsagaita wutar kuma za ta ci gaba da bayar da gudunmawa wajen ganin an tabbatar da zaman lafiya.

Ya jaddada matsayin Ankara wajen samar da ƙasar Falasɗinu mai cin gashin kanta bisa iyakokin da aka shata a shekarar 1967 da kuma Gabashin Birnin Ƙudus a matsayin babban birninta.

Da yake nuna goyon bayansa ga Falasɗinawa waɗanda suka kasance cikin uƙuba da tafka asara a shekaru biyu da suka wuce, Erdogan ya jinjina musu game da jajircewarsu da kuma martabarsu duk da mawuyacin halin da suke ciki.

Ana sa ran saka hannu kan yarjejeniyar tsagaita wuta a yakin Gaza da Trump ke jagoranta da misalin ƙarfe 0900 GMT a Masar, kamar yadda wata majiya da ke da sanayya kan lamarin ta shaida wa Reuters ranar Alhamis.

Kazalika ana sa rai yarjejeniyar za ta soma aiki da Gaza da zarar an sanya mata hannu, a cewar majiyar.

Rumbun Labarai
Turkiyya ta yi umarnin kama Firaministan Isra'ila Netanyahu da wasu mutane kan kisan kiyashi a Gaza
Turkish Airlines ya sayi hannun jari na dala miliyan 355 a kamfanin Air Europa na Spain
Erdogan ya yi Allah wadai da kashe fararen-hula a birnin Al Fasher na Sudan
Za a gudanar da tattaunawa a Istanbul kan yarjejeniyar tsagaita wutar Gaza da matsalolin jinƙai
Tsarin duniya na yanzu ya fi ba da fifiko kan iko fiye da adalci: Babban Daraktan TRT Sobaci
Hamas ba ta da nukiliya, amma Isra'ila na da su: Erdogan ya nemi Berlin ta ɗauki mataki kan Tel Aviv
Ana shirin fara taron TRT World Forum karo na 9 a Istanbul
Cikin hotuna: Yadda aka yi bukukuwa a duk faɗin kasa na cikar Ranar Jamhuriya ta Turkiyya ta 102
Turkiyya ta yi kira a tsagaita wuta nan-take a yaƙin da ake yi a birnin Al Fasher, Sudan
Turkiyya za ta mika wa dakarunta tankar yaki ta Altay da aka samar da yawa a karon farko
Kungiyar ta'addanci ta PKK ta sanar da janyewa baki ɗaya daga Turkiyya
Babu wani lissafin siyasa ko na tsaro da zai yiwu a duniya ba tare da Turkiyya ba: Erdogan
Rumfar Karfe: Fasahar Turkiyya ta cikin gida mai aiki da Ƙirƙirarriyar Basira a sabon zamanin tsaro
Shugaba Erdogan ya shirya ziyartar yankin Gulf don haɓaka alaƙar tattalin arziki da ƙawance
Turkiyya ta yi maraba da yarjejeniyar tsagaita wutar Afghanistan da Pakistan
An Fara Taron Yaki da Shara na ‘Zero Waste’ a Istanbul karkashin jagorancin Emine Erdogan
Matar Shugaban Turkiyya Emine Erdogan ta yi kira a bunkasa shigar mata cikin harkokin duniya
Cinikayya tsakanin Turkiyya da Afirka ta wuce $37b ana sa ran ta kai $40b a 2025: Minista
Turkiyya na da rawar da za ta taka a tsaron Turai, ta shirya domin aikin Gaza: Ministan Tsaro
Turkiyya ta yi maraba da amincewar majalisar dokokin TRCN kan ƙudurin samar da ƙasashe biyu