| hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
Kashim Shettima ya gana da Sakatare-Janar na MDD kan yunkurin Nijeriya na neman kujerar dindindin
Tattaunawar ta kuma shafi sauyin yanayi, da ci gaba mai ɗorewa, da haɗin gwiwar Nijeriya da shirin raya ƙasa na Majalisar Dinkin Duniya.
Kashim Shettima ya gana da Sakatare-Janar na MDD kan yunkurin Nijeriya na neman kujerar dindindin
Kashim Shettima da Antonio Guttares
26 Satumba 2025

Mataimakin Shugaban Nijeriya Kashim Shettima ya ƙara ƙaimi a yaƙin nema wa Nijeriya kujerar dindindin a kwamitin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya.

A yayin ganawarsa da Sakatare Janar na MDD, António Guterres a hedkwatar majalisar da ke New York, Shettima ya jaddada cewa Nijeriya ta cancanci samun goyon baya mai ƙarfi daga ƙasashen duniya, yana mai nuni da irin rawar da kasar ke takawa wajen samar da zaman lafiya, da dimokuradiyya, da zaman lafiyar yankin.

Tattaunawar ta kuma shafi sauyin yanayi, da ci gaba mai ɗorewa, da haɗin gwiwar Nijeriya da shirin raya ƙasa na Majalisar Dinkin Duniya.

Ministoci a tawagar Mataimakin Shugaban Ƙasar sun ce Guterres ya yaba da ci gaban da Nijeriya ta samu a fannin fasahar ƙere-ƙere, musamman yadda aka ƙaddamar da tsarin fara amfani da yare da yaruka da yawa da wata gwamnati ta taɓa kafawa a Afirka.

Mista Guterres ya tabbatar wa Nijeriya cewa za a ci gaba da ba ta tallafi.

Tun da farko, Mataimakin Shugaban Ƙasar Kashim Shettima ya kuma gana da Mataimakin Firaministan Birtaniya David Lammy, inda bangarorin biyu suka amince da zurfafa hadin gwiwa a fannonin ciniki, tsaro, da kuma ƙaura.

Har ila yau, Mataimakin Shugaban Ƙasar ya bi sahun shugabannin kasashen duniya a taron majalisar jagoranci na duniya, inda ya tabbatar da cewa hada kan dijital da karfafa matasa sun kasance a mahimmai a gun Shugaba Bola Tinubu.

 

Rumbun Labarai
Rundunar sojin Nijeriya ta kuɓutar da masu yi wa ƙasa hidima 47 daga 'yan Boko Haram a Borno
Nijeriya ta dakatar da aiwatar da harajin kashi 15% kan shigar da fetur da dizal cikin ƙasar
'Musulmai ne Boko Haram ta fara yi wa ɓarna': AU ta yi watsi da Trump kan kisan kiyashi a Nijeriya
Za mu bai wa kowane jami'in soja da ke bakin aikinsa kariya  - Ministan Tsaron Nijeriya
An kama hodar ibilis mai nauyin kilogiram 1,000 a Nijeriya
‘Yan wasan Super Eagles sun ƙaurace wa atisaye kan rashin biyansu alawus
Jiragen yaƙin Nijeriya sun kashe ‘yan ta’addan ISWAP da ɓarayin daji a Borno da wasu jihohin Arewa
Babu abin da za mu rasa idan Nijeriya ta daina hulɗa da Amurka – Sheikh Gumi
Damuwa kan kutsawar 'yan bindiga Jihar Kano
Rundunar sojin Nijeriya ta ce ta kuɓutar da mutum 86 da Boko Haram ta yi garkuwa da su
INEC ta ayyana Charles Soludo na APGA a matsayin wanda ya lashe zaɓen Gwamnan Anambra
Gwamnatin Nijeriya ta amince a ci bashin dala 396 domin inganta kiwon lafiya da ayyukan jinƙai
An gabatar da kudiri a Majalisar Dokokin Amurka don saka wa Ƙungiyoyin Miyetti Allah takunkumi
‘Kisan kiyashi ga Kiristoci: Me ya sa kurarin Trump a Nijeriya yake kan kuskure da rashin dacewa?
Majalisar Dattawan Nijeriya ta amince a ɗaure malaman makaranta shekara 14 kan cin zarafin ɗalibai
An kashe 'yan ta'adda fiye da 592 a Borno tun daga Maris din 2025 - Ministan Yada Labaran Nijeriya
ECOWAS ta yi tir da ikirarin ‘ƙarya mai hatsari’ na Amurka cewa Nijeriya ta bari ana kashe Kiristoci
Hukumar DSS a Nijeriya ta kori ma'aikatanta fiye da 100
Amurka na da ajanda a Nijeriya tana fakewa da kisan Kiristoci - Sheik Bala Lau
China na adawa da Trump kan amfani da 'addini da ‘yancin ɗan'adam' domin tsoma baki a Nijeriya