| hausa
NIJERIYA
3 minti karatu
Kotu ta hana PENGASSAN katse wa Matatar Dangote bututun gas
Mai Shari’a Subilim ya hana waɗanda aka kai ƙarar ciki har da kamfanin mai na Nijeriya NNPCL da hukumar NMDPRA da kuma hukumar NUPRC aiwatar da umarnin PENGASSAN na hana bai wa matatar Dangote ɗanyen mai da iskar gas.
Kotu ta hana PENGASSAN katse wa Matatar Dangote bututun gas
Matakin ya biyo bayan korar ma'aikata fiye da 800 da matatar ta Dangote ta yi a makon nan
30 Satumba 2025

Mai Shari’a Emmanuel Subilim na kotun masana’antu ta ƙasa da ke babban birnin Nijeriya Abuja, ya hana ƙungiyar ma’aikatan man fetur da iskar gas (PENGASSAN) aiwatar da yajin aikinta kan Matatar Man Dangote.

Da yake yanke  hukunci kan ƙarar da Matatar Dangote ta kai kotun, Mai shari’a ya hana waɗanda aka kai ƙarar, ciki har da kamfanin man Nijeriya NNPCL da hukumomi masu kula da haƙowa da dako da kuma sarrafa ɗanyen mai da iskar gas datse wa Matatar Dangote damar samun ɗanyen mai da iskar gas.

Wani babban lauya a Nijeriya, George Ibrahim, ne ya gabatar da ƙarar tare da gamsar da alƙalin da ya ba da umarnin.

Ƙungiyar PENGASSAN ce ta bayar da umarni ga ma’aikatanta da su katse duk wata hanya da matatar Dangote take samun ɗanyen fetur da iskar gas sakamakon rikicin da ya kaure a tsakaninsu bisa zargin korar ma’aikatanta da ke aiki a matatar da kuma batun zaɓin zama ‘ya’yan ƙungiyar.

Sai dai a matatar mai ta Dangote ta garzaya kotu domin hana aiwatar da matakin.

A hukuncinsa, Mai shari’a Subilim ya ce masu shigar da ƙarar sun yi daidai domin yajin aikin ma’aikatan PENGASSAN zai yi illa ga harkokin kamfanin tare da katse samar da muhimmin abu (man fetur) ga ‘yan Nijeriya.

Alƙalin ya ce abin da ya dace da adalci shi ne kotun ta hana waɗanda aka kai ƙarar domin tabbatar da zaman lafiya a ma’aikatar da kuma ƙara taimakawa wajen ci gaba da yi wa ‘yan Nijeriya muhimmiyar hidima har zuwa lokacin da za a ji asalin ƙarar.

Yayin da yake ba da umarnin hana waɗanda aka kai ƙarar ɗaukar mataki, Mai shari’a Subilim, ya bayar da umarnin cewa a kai wa waɗanda aka kai ƙarar umarnin dakatar da ɗaukar matakin nan-take. 

Ƙoƙarin sansatawa ya ci tura

Zaman da gwamnatin Nijeriya ta shirya domin yin sulhu tsakanin Matatar Dangote da ƙungiyar PENGASSAN ya kasa cim ma matsaya ranar Litin da daddare.

Zama da Ministan Ƙwadago da ayyukan yi, Muhammad Dingyadi , ya jagoranta ya haɗa masu ruwa da tsaki ciki har da shugabannin ƙungiyar PENGASSAN da wakilan Matatar Dangote da Ministan Kuɗi da daraktoci daga hukumomin NUPRC da NMDPRA.

Rahotanni dai sun ce zaman da aka yi a Abuja an fara shi ne da misalin ƙarfe 3:50 na rana maimakon ƙarfe 2: 00 da aka tsara, kuma ba gama shi ba sai bayan ƙarfe 12:00 na dare inda aka tashi ba tare da cim ma matsaya ba.

Sai dai kuma rahotanni sun ce ana ganin za a  ci gaba da tattaunawar ranar Talata da misalin ƙarfe 2:00 na rana.

 

 

Rumbun Labarai
Za mu bai wa kowane jami'in soja da ke bakin aikinsa kariya  - Ministan Tsaron Nijeriya
An kama hodar ibilis mai nauyin kilogiram 1,000 a Nijeriya
‘Yan wasan Super Eagles sun ƙaurace wa atisaye kan rashin biyansu alawus
Jiragen yaƙin Nijeriya sun kashe ‘yan ta’addan ISWAP da ɓarayin daji a Borno da wasu jihohin Arewa
Babu abin da za mu rasa idan Nijeriya ta daina hulɗa da Amurka – Sheikh Gumi
Damuwa kan kutsawar 'yan bindiga Jihar Kano
Rundunar sojin Nijeriya ta ce ta kuɓutar da mutum 86 da Boko Haram ta yi garkuwa da su
INEC ta ayyana Charles Soludo na APGA a matsayin wanda ya lashe zaɓen Gwamnan Anambra
Gwamnatin Nijeriya ta amince a ci bashin dala 396 domin inganta kiwon lafiya da ayyukan jinƙai
An gabatar da kudiri a Majalisar Dokokin Amurka don saka wa Ƙungiyoyin Miyetti Allah takunkumi
‘Kisan kiyashi ga Kiristoci: Me ya sa kurarin Trump a Nijeriya yake kan kuskure da rashin dacewa?
Majalisar Dattawan Nijeriya ta amince a ɗaure malaman makaranta shekara 14 kan cin zarafin ɗalibai
An kashe 'yan ta'adda fiye da 592 a Borno tun daga Maris din 2025 - Ministan Yada Labaran Nijeriya
ECOWAS ta yi tir da ikirarin ‘ƙarya mai hatsari’ na Amurka cewa Nijeriya ta bari ana kashe Kiristoci
Hukumar DSS a Nijeriya ta kori ma'aikatanta fiye da 100
Amurka na da ajanda a Nijeriya tana fakewa da kisan Kiristoci - Sheik Bala Lau
China na adawa da Trump kan amfani da 'addini da ‘yancin ɗan'adam' domin tsoma baki a Nijeriya
Naira da hannayen-jari Nijeriya sun faɗi sakamakon barazanar da Trump ya yi ta kai hari ƙasar
Jami'an tsaron Nijeriya sun hallaka 'yan bindiga 19 a Jihar Kano
Yadda barazanar da Trump ya yi kan aika sojoji Nijeriya ta tayar da ƙura