| hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
An kulle NNPC da NUPRC da NMDPRA saboda yajin aikin PENGASSAN a Nijeriya
Kazalika, harkoki a hedikwatar hukumar NMDPRA mai kula da yadda ake dakon ɗanyen mai a tsakiyar Abuja inda ake yawan hada-hada sun tsaya cak saboda yajin aikin.
An kulle NNPC da NUPRC da NMDPRA saboda yajin aikin PENGASSAN a Nijeriya
Ana fargabar tsadar mai a Nijeriya sakamakon yajin aikin
29 Satumba 2025

Yajin aikin da ƙungiyar manyan ma’aikatan man fetur da iskar ta Nijeriya (PENGASSAN) ta fara ranar Litinin ya katse aiki a mahimman ma’aikatu da hukumomi na fannin man fetur ciki har da kamfanin man Nijeriya NNPC da hukumomin da ke sa ido kan harkoki haƙowa da rabawa da kuma tace mai.

Yajin aikin, wanda ya biyo bayan umarnin kwamitin zartarwar ƙungiyar, ya sa mambobin ƙungiyar a fadin ƙasar sun ƙaurace wa aiki, lamarin da ya kulle mahimman ma’aikatu da hukumomin da ke jagorantar fannin man Nijeriya.

Rahotanni daga Nijeriya sun ce hedikwatar hukumar NUPRC mai kula da haƙo mai a ƙasar ta kasance a kulle ranar Litinin, inda ma’aikata suka kasa iya shiga hedikwatar.

Jami’an tsaro da ke aiki sun tabbatar da cewa babu ma’aikacin da aka bai wa damar shiga, bisa umarnin ƙungiyar.

Kazalika, harkoki a hedikwatar hukumar NMDPRA mai kula da yadda ake dakon ɗanyen mai a tsakiyar Abuja inda ake yawan hada-hada sun tsaya cak saboda yajin aikin.

Da yake tabbatar da lamarin, shugaban PENGASSAN a hukumar NMDPRA, Tony Iziogba, ya bayyana cewa ƙungiyar ta yi nasarar tabbatar da aiwatar da yajin aikin 100 bisa 100, lamarin da ya hana ma’aikata da baƙi shiga ofishin.

Ya ƙara da cewa abokanan aikinsa sun tabbatar da cewa an bi umarnin yajin aikin 100 bisa 100 a hedikwatar kamfanin man Nijeriya NNPCL da sauran hukumomi masu ruwa da tsaki.

PENGASSAN ta ce yajin aikin ya zama dole ne bayan zargin da ta yi na kora ba bisa ƙa’ida ba da aka yi wa ma’aikata 800 a Matatar Man Dangote.

Umarnin ƙungiyar na dakatar da bayar da ɗanyen mai da iskar gas ga Matatar Man Dangote ya saka damuwa a fannin na makamashin Nijeriya inda kamfanonin da ake sayar da mai ke gargaɗin cewa za a samu tsaiko mai tsanani wajen samar da mai, lamarin da zai sa a ƙara farashin mai.

Rumbun Labarai
Za mu bai wa kowane jami'in soja da ke bakin aikinsa kariya  - Ministan Tsaron Nijeriya
An kama hodar ibilis mai nauyin kilogiram 1,000 a Nijeriya
‘Yan wasan Super Eagles sun ƙaurace wa atisaye kan rashin biyansu alawus
Jiragen yaƙin Nijeriya sun kashe ‘yan ta’addan ISWAP da ɓarayin daji a Borno da wasu jihohin Arewa
Babu abin da za mu rasa idan Nijeriya ta daina hulɗa da Amurka – Sheikh Gumi
Damuwa kan kutsawar 'yan bindiga Jihar Kano
Rundunar sojin Nijeriya ta ce ta kuɓutar da mutum 86 da Boko Haram ta yi garkuwa da su
INEC ta ayyana Charles Soludo na APGA a matsayin wanda ya lashe zaɓen Gwamnan Anambra
Gwamnatin Nijeriya ta amince a ci bashin dala 396 domin inganta kiwon lafiya da ayyukan jinƙai
An gabatar da kudiri a Majalisar Dokokin Amurka don saka wa Ƙungiyoyin Miyetti Allah takunkumi
‘Kisan kiyashi ga Kiristoci: Me ya sa kurarin Trump a Nijeriya yake kan kuskure da rashin dacewa?
Majalisar Dattawan Nijeriya ta amince a ɗaure malaman makaranta shekara 14 kan cin zarafin ɗalibai
An kashe 'yan ta'adda fiye da 592 a Borno tun daga Maris din 2025 - Ministan Yada Labaran Nijeriya
ECOWAS ta yi tir da ikirarin ‘ƙarya mai hatsari’ na Amurka cewa Nijeriya ta bari ana kashe Kiristoci
Hukumar DSS a Nijeriya ta kori ma'aikatanta fiye da 100
Amurka na da ajanda a Nijeriya tana fakewa da kisan Kiristoci - Sheik Bala Lau
China na adawa da Trump kan amfani da 'addini da ‘yancin ɗan'adam' domin tsoma baki a Nijeriya
Naira da hannayen-jari Nijeriya sun faɗi sakamakon barazanar da Trump ya yi ta kai hari ƙasar
Jami'an tsaron Nijeriya sun hallaka 'yan bindiga 19 a Jihar Kano
Yadda barazanar da Trump ya yi kan aika sojoji Nijeriya ta tayar da ƙura