SIYASA
2 minti karatu
Za a ƙaddamar da shirin bayar da lasisin bindiga na intanet a Ghana
"Za a haɗa dukkan lasisin bindiga da katin [shaidar ɗan ƙasa] na Ghana domin sauƙaƙa bibiyar waɗanda suka mallaki bindigogi lamarin da zai rage yawan aikata laifuka a ƙasar, in ji ministan tsaron cikin gida.
Za a ƙaddamar da shirin bayar da lasisin bindiga na intanet a Ghana
Rundunar ’yan sandan Ghana ta ce ta tara bayanan duk masu lasisi a komfuta kuma tana wayar da kansu domin su sabunta lasisinsu kan lokaci
1 Oktoba 2025

Ma’aikatar tsaron cikin gida ta ƙasar Ghana za ta ƙaddamar da lasisin bindiga na intanet daga watan Disambar shekarar 2025 domin inganta sa ido kan mallakar bindiga da kuma rage mallakar bindiga ba bisa ƙ’ida ba a ƙasar.

Ministan tsaron cikin gida na Ghana, Muntaka Mohammed Mubarak ne ya shaida wa kwamitin binciken kuɗi a majalisar dokokin ƙasar cewa wata kafa ta intanet ce za ta maye gurbin tsarin takarda da ake amfani a halin yanzu domin inganta sabunta lasisi.

Ya ce sabon tsarin zai bai wa masu lasisi damar sabunta lasisinsu ta intanet kuma su biya kuɗi ta wayar salula.

Kazalika ya ce tsarin zai tura wa mutane saƙon tuni watanni uku gabanin ƙarewar lasisinsu tare da hana waɗanda ke da tarihin aikata laifi sabunta lasisinsu.

"Za a haɗa dukkan lasisin bindiga da katin [shaidar ɗan ƙasa] na Ghana domin sauƙaƙa bibiyar waɗanda suka mallaki bindigogi lamarin da zai rage yawan aikata laifuka a ƙasar, in ji ministan tsaron cikin gida.

Bayanin ministan ya biyo bayan ƙorafin da wata mambar kwamitia, Mis Helen Adjoa Ntoso, ta nuna ne inda ta ce bindigogi 606 ne a hannun fararen-hula ba bisa ƙa’ida ba saboda masu bindigogin ba su sabunta lasisinsu ba.

Babban Sufeto Janar na ’yan sandan ƙasar, Mista Christian Tetteh Yohuno, ya ce rundunar ‘yan sandan ƙasar ta tara bayanan duk masu lasisi a komfuta kuma tana wayar da kansu domin su sabunta lasisinsu kan lokaci.

Ya bayyana cewa lasisi na kai wa shekara ɗaya ne, amma da yawa daga cikin masu riƙe da su ba sa sabunta su har sai lokacin da matsala ta auku.

 Mubarak ya ce tsarin komfuta zai inganta sa ido kan lasisin da suka ƙare da kuma ƙarfafa ikon ‘yan sanda wajen ƙwace makaman da ake riƙe da su ba bisa ƙa’ida ba.

 

Rumbun Labarai
Kutungwilar Netanyahu kan tsagaita wuta a Gaza ita ce ci gaba da kashe Falasdinawa
Zaben Tanzania: Intanet ya katse sannan zanga-zanga ta barke a ranar zabe
Masu nazarin kayan tarihi sun gano kisan gillar Faransa a wata makabartar Senegal
Mahama ya hana ministoci bayyana manufofin gwamnatin Ghana sai da izinin majalisar ministoci
Shugaban Sudan al Burhan ya ce ‘sojojin ƙasar sun janye’ daga Al Fasher
Hamas na aiki da yarjejeniyar tsagaita wuta amma Isra'ila na ci gaba da karya ta, in ji Erdogan
Ghana tana alhinin mutuwar matar tsohon shugaban ƙasar, Nana Konadu Agyeman-Rawlings
Kotu a Bangladesh ta tura manyan hafsoshin soji gidan yari a wata shari’a ta tarihi
Tsohon shugaban Faransa Nicolas Sarkozy ya fara zaman  gidan kaso kan karɓar kuɗin a wurin Gaddafi
Firaministan Falasɗinu ya bayyana shirin ware dala biliyan 65 don sake gina Gaza
Tsohon Firaministan Kenya Raila Odinga ya mutu a India
Shugaban Madagascar na ɓuya a wani 'wuri mai aminci' bayan mummunar zanga-zangar da ta ɓarke a ƙasar
Yadda diflomasiyyar Erdogan na Turkiyya ta taimaka wajen cim ma tsagaita wuta a Gaza
Burkina Faso ta kama ma’aikatan jinƙai bisa zargin leƙen asiri
Shekaru biyu na kisan kiyashin Isra’ila a Gaza: Yadda Amurka ke kare Netanyahu daga tuhuma
Swahili ne mafita ga Gabashin Afirka ba Faransanci ba
ICC: Yaudara daga wadanda suka kafa ta, mafaka ga mambobin ƙasashen Afirka
Fayyaceccen bayanin Erdogan a MDD: Gaza, 'ƙasar Isra'ila', da makomar yankin
Mene ne daftarin Babban Zauren MDD kan mafitar samar da ƙasashe biyu da ƙarara ya yi watsi da Hamas?
INEC ta buƙaci a hukunta duk wanda ya fara kamfen ɗin 2027 kafin lokaci