Ga manyan batutuwa huɗu daga jawabin Sarkin Qatar a taron UNGA
DUNIYA
3 minti karatu
Ga manyan batutuwa huɗu daga jawabin Sarkin Qatar a taron UNGASarkin Qatar, Sheikh Tamim bin Hamad Al Thani ya faɗa wa Majalisar Dinkin Duniya cewa ayyukan Isra'ila suna kassara ƙoƙarin tsagaita wuta, kuma ya zarge ta da ƙoƙarin mayar da Gaza wajen da ba za a iya rayuwa cikinsa ba.
Sarkin Qatar ya sha alwashin ci gaba da matsawar diflomasiyya don kawo ƙarshen yaƙin Gaza, duk da harin Isra'ila a Doha.
24 Satumba 2025

Sarkin Qatar ya faɗa wa shugabannin duniya cewa ƙasarsa tana ci gaba da ƙoƙarinta na diflomasiyya don kawo ƙarshen yaƙin Gaza duk da mummunan harin Isra’ila kan shugabannin Hamas a ƙasar wadda ke yankin Gulf.

Da yake jawabi ga babban taron Majalisar Ɗinkin Duniya a yammacin Talata, Sarki Sheikh Tamim bin Hamad Al Thani ya yi tir da harin Isra’ila "na cin amana" a tsakiyar unguwannin mutane a birnin Doha, inda Hamas ke da ofishin tuntuɓa.

Ƙalubale kan diflomasiyya

Qatar, tare da Masar da Amurka, sun jagoranci ƙoƙarin samar da cikakken matakin tsagaita wuta tsakanin Isra’ila da Hamas, inda aka gudanar da zagayen diflomasiyya a Doha, wanda bai yi nasara ba.

Ya faɗa wa Babban Zauren Taron cewa, "Saɓanin iƙirarin firaministan Isra’ila, wannan hari ba ya cikin halastaccen haƙƙin bibiyar masu ta’addanci" kuma ya "kassara ƙoƙarin diflomasiyya da ke muradin kawo ƙarshen kisan ƙare-dangi kan al’ummar Gaza".

Ya ƙara da cewa, "Za mu yi aikin diflomasiyya yayin da abokan gabarmu suke ganin sauƙin amfani da makamai".

"Za mu ci gaba da ƙoƙarinmu na haɗin-kai, tare da haɗin gwiwa da Masar da Amurka."

Kisan kiyashi

Sarki Al Thani ya zargi Isra’ila da amfani da yaƙi a matsayin makami don mayar da Gaza mara zaunuwa, inda take lalata gidaje, makarantu, asibitoci, da kayan more rayuwa don tilasta ƙauracewa.

Ya yi gargaɗin cewa wannan yaƙin ba a Gaza ya tsaya ba, inda ya alaƙanta shi da babban burin kankane Gaɓar Yamma, don sauya matsayar da ake da ita a Al-Aqsa Mosque, ɗaya cikin mafi darajar wurare ga Musulmai a duniya.

Ya ce ayyukan Isra’ila sun kai matakin kisan ƙare-dangi kuma ya nuna hujjar manufar tsarinta na “Faɗaɗa Ƙasar Isra’ila,” wanda ke sanya zaman lafiya ya ƙi yiwuwa" Manufarsu ita ce ruguza Gaza don su hana su rayuwa. Sakamakon haka, shugaban Isra’ila yana so ya ci gaba da yaƙi."

Amincewa da Ƙasar Falasɗinu

Sarkin Qatar ɗin ya kuma jaddada kiransa na kafa ƙasashe biyu bisa iyakokin 1967 da kuma sanya Gabashin Jerusalem a matsayin babban birnin Falasɗinu.

Ya yaba wa ƙasashen da suka riga suka amince da ƙasar Falasɗinu, yana mai cewa wannan matakin yana nuna ƙaƙƙarfan saƙon cewa: wannan matsanancin zalunci ba zai goge mataki nagari ba.

Ya nemi sauran ƙasashe su biyo sahu, kuma ya yi gargaɗin cewa yin shiru kawai yana ƙarfafa cigaba da kisan kiyashi ne da mamaya.

Tasirin Ƙasashen Duniya

Sarkin Qatar, Emir Al Thani ya bayyana Doha a matsayin amintacciyar mai shiga tsakani a faɗin duniya.

Ya yi nuni da rawarta a warware rikici, daga Ukraine zuwa Afirka, ciki har da ƙoƙarin samar da zaman lafiya a Jumhoriyar Dimukuraɗiyyar Congo.

Ya kuma sha alwashin tallafa wa neman daidaita lamura a Syria, Lebanon, da Sudan, inda kuma ya bayyana aikin Qatar na shirya taron tattaunawa ta hanyar manyan bukukuwa kamar na shekara mai zuwa, na bikin Social Development Summit da kuma yunƙurin karɓar baƙuncin Wasannin Olympics na 2036.

Ya ce, “Wasanni wata mahaɗa ce ta zaman lafiya da fahimtar juna.”

Rumbun Labarai
COP30: Manyan masu gurbata muhalli na duniya ba su je taron sauyin yanayi na Brazil ba
Rasha ta ce tana sa ido kan Nijeriya bayan barazanar da Trump ya yi ta kai hari kasar
Zohran Mamdani: Matashi Musulmi na farko ya lashe zaɓen Magajin Birnin New York
Yadda amfani da magungunan antibiotic barkatai ya sa cututtuka suka zama makamai
Rundunar Sojin Ruwan Pakistan ta kama mugwayen ƙwayoyi na dala biliyan ɗaya a Tekun Arebiya
An gano sauro a karon farko a ƙasar Iceland
Yadda hukumomi a India suke farautar Musulmai da suke cewa 'Ina son Annabi Muhammad'
Putin ya gargaɗi Trump cewa bai wa Ukraine makamai mai linzamin Tomahawk zai jawo matsala tsakaninsu
Abin da muka sani game da mummunar arangamar kan iyaka tsakanin sojin Pakistan da Afganistan
Waiwayen 1903: An taɓa yi wa Yahudawa tayin Afirka, kamar yadda ake so a mayar da Falasɗinawa yanzu
An naɗa Sarah Mullally mace ta farko Shugabar Cocin Ingila
Yadda mutuwar ɓauna a turmutsutsu ke sauya salon farautar manyan namun dawa
An tsinci gawar jakadan Afirka ta Kudu a Faransa a wajen otal a birnin Paris
Babban Alkalin Kotun Amurka ya dakatar da umarnin Trump na korar ma’aikatan VOA
UNGA: Yadda ta kaya a taron 'nuna wa juna yatsa da huce haushi' na Majalisar Dinkin Duniya
Yadda jami'an diflomasiyyar duniya suka fice daga Zauren UNGA yayin da Netanyahu zai yi jawabi
Jawabin Trump a taron MDD ya fito da sakamakon nuna ƙyamar Musulunci a duniya
An yanke wa tsohon Shugaban Faransa Sarkozy hukuncin shekara biyar a gidan yari
UNGA 80: Trump ya yi alkawarin hana Isra'ila shirin ƙwace Yammacin Kogin Jordan
Muradun Ƙungiyar G7 a UNGA sun haɗa da ƙara tallafa wa Ukraine da neman tsagaita wuta a Gaza