AFIRKA
2 minti karatu
Shugaba Mahama ya gabatar da sunan Paul Baffoe-Bonnie a matsayin alƙalin alƙalan Ghana
Kazalika sanawar ta ce Mai Shari’a Baffoe-Bonnie ya ba da gudunmawa mai yawa a fannin shari’ar Ghana.
Shugaba Mahama ya gabatar da sunan Paul Baffoe-Bonnie a matsayin alƙalin alƙalan Ghana
A farkon wannan watan ne Shugaba Mahama ya kori alƙaliyar alƙalan ƙasar Gertrude Araba Esaaba Sackey Torkornoo, daga muƙaminta.
24 Satumba 2025

Shugaban Ghana John Mahama ya gabatar da sunan Paul Baffoe-Bonnie ga majalisar magabata ta ƙasar a matsayin alƙalin alƙalan Ghana kamar yadda sashi na 144(1) ya tanada.

Kamfanin dillancin labaran ƙasar ya ambato wata sanarwar da mai magana da yawun shugaban ƙasar, Felix Kwakye Ofosu, ya fitar na cewa mai shari’a Baffoe-Bonnie ya yi aiki tuƙuru bisa gaskiya a alƙalancin da ya yi a babbar kotu da kotun ɗaukaka ƙara da wanda yake a kotun ƙoli a yanzu.

Kazalika sanawar ta ce Mai shari’a Baffoe-Bonnie ya ba da gudunmawa mai tarin yawa a fannin shari’ar Ghana.

Mai magana yawun shugaban ya ce ilimi da rashin son kansa ya sa ana girmama shi a ɓangaren alƙalai da lauyoyi da ma fannin shari’a gaba ɗaya.

Ya ce ƙwarewarsa da kuma daɗewarsa a alƙalanci sun sa ya cancanta sosai ya riƙe kujerar alƙalin alƙalan ƙasar.

Kazalika sanarwar ta ce alƙalin alƙalan ya fara aiki ne a matsayin muƙaddashin alƙalin alƙalan ƙasar tun ranar 22 ga wata Afrilu.

 

Korar alƙaliyar alƙalan Ghana

A farkon wannan watan ne Shugaba Mahama ya kori alƙaliyar alƙalan ƙasar Gertrude Araba Esaaba Sackey Torkornoo, daga muƙaminta.

Shugaban ya sauke alƙaliyar ne bayan an same ta da laifin yin amfani da matsayinta wajen aikata ba daidai ba.

Kamfanin dillancin labaran ƙasar ya ruwaito cewa Shugaba Mahama ya ɗauki matakin ne bayan ya dogara kan sashe na 146(9) na kundin tsarin mulkin ƙasar na shekarar 1992.

Wannan ya biyo bayan samun sakamakon binciken kwamitin da aka kafa a ƙarƙashin sashe na 146 (6) na kundin tsarin mulkin ƙasar domin bincike kan ƙorafin da wani ɗan ƙasar ta Ghana mai suna Mista Daniel Ofori ya shigar a kan alƙaliyar alƙalan.

Wata sanarwa da Mista Felix Kwakye Ofosu, mai magana da yawun shugaban ƙasar kuma ministan sadarwar gwamnati ya sanya wa hannu a Accra, a babban birnin ƙasar  ta ce shugaban ƙasar ya ɗauki wannan matakin ne bayan kwamitin ya tabbtar da dalilin cire ta daga muƙaminta.

Ranar Litinin ne dai Shugaban ƙasar ya karɓi rahoton kwamitin da ya yi nazari kan ƙarar neman a kori alƙaliyar alƙalai Gertrude Araba Esaaba Sackey Torkornoo.

Maisharia Gabriel Scott Pwamang na kotun ƙolin ƙasar da ya jagoranci kwamitin ne ya gabatar da rahoton kwamitin ga shugaban ƙasar a fadar gwamnatin ƙasar da ke Accra.

 

 

Rumbun Labarai
Sojojin Sudan sun harbo jirgi maras matuƙi na RSF a Kordofan ta Arewa
Dakarun Nijar sun cafke muggan makamai da aka yi safararsu daga Libya, sun kama masu safarar ƙwayoyi
RSF ta Sudan ta kai hare-hare a Jihar Khartoum da birnin Atbara bayan amincewa da tsagaita wuta
Paul Biya na Kamaru: Shugaban da ya fi tsufa a duniya ya sha rantsuwar kama aiki karo na takwas
Hatsarin mota ya yi ajalin fiye da mutum 1,000 a Nijar a shekarar 2023, fiye da 12,000 sun jikkata
Sabbin hotunan tauraron dan'adam sun gano alamun 'kaburburan bai-daya a El-Fasher a Sudan
MDD ta yi gargaɗin cewa yaƙin Sudan na gurgunta tattalin arzikin Sudan ta Kudu
Trump ya ce bai kamata Afirka ta Kudu ta kasance cikin G20 ba, ba zai je taronta a Johannesburg ba
'Yan Sudan sun ba da mummunan labarin yi wa mata fyade yayin da suke tserewa daga Al Fasher
An kashe mutane 40 a harin da aka kai wa taron jana'iza a yankin Kordofan na Sudan: MDD
Yadda biranen Afirka mafiya tsafta suke bayyana sauyin da ake samu a nahiyar
Sojojin Ruwa na Ghana sun kama ‘yan Nijeriya 10 da suka ɓuya a jirgin ruwan Panama a Tema
Harin jirgin sama maras matuƙi na RSF ya kashe mutane da dama a lardin Kordofan na Arewa a Sudan
Fiye da mutum 1,500 sun rasa matsugunansu a Sudan sakamakon taɓarɓarewar tsaro: MDD
Dakarun RSF sun kashe mata 300, sun yi wa 25 fyaɗe cikin awa 48 a Al Fasher – Minista
Amurka ta buƙaci a tattauna domin kawo ƙarshen yaƙin Sudan, ba amfani da ƙarfin soja ba
Ana fargabar dubban mutane na cikin 'mummunan hatsari' a birnin Al Fasher na Sudan da RSF ta ƙwace
Shugabar Tanzania Samia Hassan ta lashe zaɓen ƙasar da kashi 97.66 cikin 100
Tchiroma Bakary: Sojojin Kamaru sun yi wa jagoran 'yan adawar kasar rakiya zuwa wuri mai 'aminci'
Kudirin 1325 ya cika shekara 25: Me ya sa dole Afirka ta jagoranci samar da zaman lafiya a duniya