| hausa
AFIRKA
1 minti karatu
DRC ta yanke wa tsohon Shugaba Joseph Kabila hukuncin kisa
Wata kotun sojoji a Jamhuriyar Dimokuradiyyar Kongo ta yanke wa tsohon Shugaban kasar Joseph Kabila hukuncin kisa a bayan idonsa, bisa samunsa da laifuka, ciki har da laifukan yaƙi.
DRC ta yanke wa tsohon Shugaba Joseph Kabila hukuncin kisa
Joseph Kabila served as DRC's president from 2001 to 2019. / Photo: Reuters
30 Satumba 2025

Wata kotun soja a Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo ta yanke wa tsohon Shugaban Ƙasar Joseph Kabila hukuncin kisa a bayan idonsa, sakamakon samunsa da laifuffuka da suka haɗa da laifukan yaƙi.

Laftanar Janar Joseph Mutombo Katalayi, wanda ya jagoranci kotun ta soja a babban birnin ƙasar, ya bayyana a ranar Talata cewa, an samu Kabila da laifufuka daban-daban, ciki har da cin amanar ƙasa, da laifukan cin zarafin bil'adama, da kisan kai, da fyade, da azabtarwa, da tayar da ƙayar baya.

Kabila ya shafe kusan shekaru ashirin yana mulki kuma ya sauka daga mulki ne kawai bayan mummunar zanga-zangar adawa da gwamnatinsa.

Tun daga ƙarshen shekarar 2023, Kabila ya koma Afirka ta Kudu da zama, duk da cewa ya bayyana a Goma, wani yanki da 'yan tawaye ke iko da shi a gabashin Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo, a watan Mayu.

Rumbun Labarai
Sojojin Sudan sun daƙile harin RSF kan filin jirgin sama da dam a arewacin ƙasar
Rubio ya nemi a daina bai wa RSF makamai, ya ɗora wa rundunar laifi kan kashe-kashe a Al Fasher
Dalilin da ya sa TikTok ya goge bidiyoyi miliyan 1.5 da 'yan Uganda suka wallafa
Mutum 12 sun mutu a turmutsutsun neman aikin soja a Ghana – Rahotanni
Mahaucin Al Fasher: Yadda hotonsa ya zama alamar bakin cikin Sudan
UN Women: Mata da 'yan mata 11M suna fama da matsanancin ƙarancin abinci a Sudan sakamakon yaƙi
WHO ta bayyana damuwa kan karuwar masu ciwon siga a Afirka
Kisan kare dangi a boye da bayyane: Gushewar jinkai a Al Fasher
An ba da belin dan Gaddafi bayan da ya shafe shekaru 10 a tsare a Lebanon
Gwamnatin Trump 'ta aika wa Equatorial Guinea dala miliyan 7.5' don ta karɓi waɗanda Amurka ta kora
Ƙasashe fiye da 20 sun yi Allah wadai da RSF kan kashe-kashen da take yi a Sudan
Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya ya yi kira da a dakatar da zubar da jini a Sudan
Paul Biya na Kamaru: Dan siyasar da zai ci gaba da yin mulki har sai ya kai shekara 99?
Hare-haren RSF sun kori ƙarin dubban mutane daga Darfur da Kordofan na Sudan
RSF ta binne gawawwaki a kabarin bai-ɗaya, ta ƙone wasu domin 'ɓoye laifukan yaƙi': Likitocin Sudan
Sojojin Sudan sun harbo jirgi maras matuƙi na RSF a Kordofan ta Arewa
Dakarun Nijar sun cafke muggan makamai da aka yi safararsu daga Libya, sun kama masu safarar ƙwayoyi
RSF ta Sudan ta kai hare-hare a Jihar Khartoum da birnin Atbara bayan amincewa da tsagaita wuta
Paul Biya na Kamaru: Shugaban da ya fi tsufa a duniya ya sha rantsuwar kama aiki karo na takwas
Hatsarin mota ya yi ajalin fiye da mutum 1,000 a Nijar a shekarar 2023, fiye da 12,000 sun jikkata