| hausa
AFIRKA
2 minti karatu
UNGA 80: Nijar ta ce dole Faransa ta 'ɗauki alhakin laifukan da ta yi' mata tun daga shekarar 1899
Firaministan Jamhuriyar Nijar Ali Lamine Zeine, a jawabinsa a Babban Taron MDD, ya zargi Faransa da "haddasa rashin zaman lafiya" a ƙasashen Sahel inda take ɗaukar nauyin "'yan ta'adda" tare da tunzura rikici a ƙasarsa da maƙotanta.
UNGA 80: Nijar ta ce dole Faransa ta 'ɗauki alhakin laifukan da ta yi' mata tun daga shekarar 1899
Lamine Zeine Ali Mahaman ya zargi Faransa da haddasa tashin hankali a Nijar, a jawabinsa na UNGA. [MDD]
28 Satumba 2025

Firaministan Jamhuriyar Nijar Ali Lamine Zeine, ya caccaki Faransa kan yin amfani da ƙungiyoyin “ta’addanci” domin tayar da rikici da haddasa rashin tsaro a ƙasarsa da maƙotanta na yankin Sahel, inda ya buƙaci mahukunta a Paris su "tuna tare da ɗaukar alhakin laifukan da suka aikata” a Nijar tun daga shekarar 1899.

"Tun lokacin da muka fatattaki sojojinsu daga [Nijar] a 2023, gwamnatin Faransa take kitsa wani shiri na ƙarƙashin ƙasa domin wargaza ƙasata," in ji Ali Lamine Zeine a jawabin da ya gabatar a gaban Babban Taron MDD [UNGA] ranar Asabar.

Kazalika ya zargi Faransa da “bayar da horo da kuɗi da kuma makamai ga ‘yan ta’adda” tare da yunƙurin haifar da “rikicin ƙabilanci” a Jamhuriyar Nijar da yankin Sahel.

Firaministan na Nijar ya ƙara da cewa mahukunta a Paris sun ƙaddamar da wani kamfe na watsa “labaran ƙarya da haddasa husuma” da zummar ɓata ƙasarsa da shugabanninta da hukumominta a idanun duniya.

Lamine Zeine ya shaida wa taron UNGA cewa Faransa tana rura wutar rikicin “siyasa tsakanin ƙasata da kuma wasu maƙotanmu," inda ya ƙara da cewa Faransa tana hana Nijar aiwatar da ayyukan ci-gaba tare da hana hukumomin kuɗinta sakat.

"Wannan ya haɗa da ƙiyayyar da Faransa take nuna mana wajen aiwatar da ayyukan ci-gaba ta hanyar hana masu son zuba jari na ƙasashen duniya irin su ADB da Asusun Bayar Da Lamuni na Duniya (IMF) da Bankin Duniya a ƙasarmu," in ji shi.

Ya ce abubuwan da suke faruwa a yankin Sahel, musamman a Nijar, sun samo asali ne sakamakon dalilai da dama.

"Da farko, har yanzu ba a warware batun mulkin mallaka ba. ‘Yan ƙasar Nijar ba su manta da azabtarwa da suka fuskanta ba sakamakon mulkin mallaka. Fitattu daga cikinsu su ne ‘yan mulkin mallaka na Voulet-Chanoine da kuma mamayar soji wadda ta haddasa gagaruman kashe-kashe a Tera, Djoundjou, Doutchi, Konni, Tessaoua da Zinder," a cewar Lamine Zeine.

Babban aikin ‘yan mulkin mallaka na Voulet-Chanoine shi ne ƙwace Yankin Chadi tare da haɗa ƙasashen Yammacin Afirka da Faransa ta mamaye ƙarƙashin tsari guda. An ƙaddamar da shirin ne daga Senegal a shekarar 1898.

Firaministan na Nijar ya ce yana "wayar da kan ƙasashen duniya domin ɗauki mataki game da waɗanna dakarun azabtarwa, waɗanda tun ƙarni na 19 ba a kwance musu ɗamara ba, kuma suna ci gaba da ƙaddamar da yaƙi a ƙasata."

Rumbun Labarai
Mahaucin Al Fasher: Yadda hotonsa ya zama alamar bakin cikin Sudan
UN Women: Mata da 'yan mata 11M suna fama da matsanancin ƙarancin abinci a Sudan sakamakon yaƙi
WHO ta bayyana damuwa kan karuwar masu ciwon siga a Afirka
Kisan kare dangi a boye da bayyane: Gushewar jinkai a Al Fasher
An ba da belin dan Gaddafi bayan da ya shafe shekaru 10 a tsare a Lebanon
Gwamnatin Trump 'ta aika wa Equatorial Guinea dala miliyan 7.5' don ta karɓi waɗanda Amurka ta kora
Ƙasashe fiye da 20 sun yi Allah wadai da RSF kan kashe-kashen da take yi a Sudan
Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya ya yi kira da a dakatar da zubar da jini a Sudan
Paul Biya na Kamaru: Dan siyasar da zai ci gaba da yin mulki har sai ya kai shekara 99?
Hare-haren RSF sun kori ƙarin dubban mutane daga Darfur da Kordofan na Sudan
RSF ta binne gawawwaki a kabarin bai-ɗaya, ta ƙone wasu domin 'ɓoye laifukan yaƙi': Likitocin Sudan
Sojojin Sudan sun harbo jirgi maras matuƙi na RSF a Kordofan ta Arewa
Dakarun Nijar sun cafke muggan makamai da aka yi safararsu daga Libya, sun kama masu safarar ƙwayoyi
RSF ta Sudan ta kai hare-hare a Jihar Khartoum da birnin Atbara bayan amincewa da tsagaita wuta
Paul Biya na Kamaru: Shugaban da ya fi tsufa a duniya ya sha rantsuwar kama aiki karo na takwas
Hatsarin mota ya yi ajalin fiye da mutum 1,000 a Nijar a shekarar 2023, fiye da 12,000 sun jikkata
Sabbin hotunan tauraron dan'adam sun gano alamun 'kaburburan bai-daya a El-Fasher a Sudan
MDD ta yi gargaɗin cewa yaƙin Sudan na gurgunta tattalin arzikin Sudan ta Kudu
Trump ya ce bai kamata Afirka ta Kudu ta kasance cikin G20 ba, ba zai je taronta a Johannesburg ba
'Yan Sudan sun ba da mummunan labarin yi wa mata fyade yayin da suke tserewa daga Al Fasher