AFIRKA
3 minti karatu
Amurka ta cire takunkumin biza kan Ghana bayan cim ma yarjejeniya kan karɓar waɗanda Trump ke kora
A farkon watan nan ne Shugaban Ghana John Dramani Mahama ya sanar da cewa ƙasarsa za ta rinƙa karɓar ‘yan Yammacin Afirka da Gwamnatin Trump ta kora.
Amurka ta cire takunkumin biza kan Ghana bayan cim ma yarjejeniya kan karɓar waɗanda Trump ke kora
“Takunkuman biza da Amurka ta ƙaƙaba wa Ghana” an “janye su,” in ji Ministan Harkokin Wajen Ghana, Samuel Okudzeto Ablakwa. / AP
9 awanni baya

Amurka ta janye takunkumin biza da ta ƙaƙaba wa Ghana, in ji Ministan Harkokin Wajen Ghana a ranar Juma’a, yayin da ƙasar ta Yammacin Afirka ke zama cibiyar karɓar 'yan gudun hijira da aka kora a ƙarƙashin matakan hana shige da fice na Shugaba Donald Trump.

A farkon wannan watan, Shugaban Ghana John Mahama ya bayyana cewa ƙasar tana karɓar yammacin Afirka da aka kora daga Amurka.

Shugaba Donald Trump na Amurka ya sanya tsarin korar mutane zuwa ƙasashen da ba su da alaƙa da su ko ‘yan uwa a can a matsayin wani muhimmin ɓangare na manufofin hana shige da fice.

Duk da haka, Accra ta jaddada cewa ba ta samu wani abu a madadin karɓar waɗannan 'yan gudun hijirar ba, duk da cewa Mahama ya amince cewa an yi yarjejeniyar yayin da dangantaka ke ƙara tsanani, tare da Washington a daidai lokacin da take ƙaƙaba haraji da takunkumin biza a watannin baya-bayan nan.

“Takunkuman biza da Amurka ta ƙaƙaba wa Ghana” an “janye su,” in ji Ministan Harkokin Wajen Ghana, Samuel Okudzeto Ablakwa.

‘Labari mai dadi’

A cikin wani rubutu a X, Ablakwa ya bayyana cewa “labari mai dadi” ya fito ne daga jami’an Amurka a gefen taron Majalisar Dinkin Duniya. Ya ce wannan sauyin ya biyo bayan “watanni na tattaunawar diflomasiyya a matakin koli.”

A watan Yuni, Amurka ta sanar da takunkumin biza ga mafi yawan 'yan ƙasashen Kamaru, Habasha, Ghana da Nijeriya, inda aka takaita su zuwa watanni uku da izinin shiga sau ɗaya kawai.

“Yanzu 'yan Ghana za su iya samun biza ta tsawon shekaru biyar tare da damar shiga fiye da sau ɗaya tare da wasu fa'idojin ofishin jakadanci,” in ji Ablakwa.

Akalla mutum 14 daga Yammacin Afirka aka tura Ghana tun farkon watan Satumba, duk da cewa ba Accra ko Washington ba su bayyana cikakkun bayanai game da haka ba.

Dukkaninsu sun samu kariya daga kotunan shige da fice na Amurka kan korar su zuwa ƙasashensu na asali, in ji lauyoyinsu, duk da cewa Ghana ta tura aƙalla mutum huɗu zuwa ƙasashensu na asali, a cewar wata ƙididdigar AFP.

An tura su Togo

Bayan shafe makonnia tasare a Ghana, inda ake zargin suna tsare ne a ƙarƙashin kulawar sojoji kuma a cikin yanayi mara kyau, mutane takwas zuwa goma daga cikin waɗanda aka kora an tura su Togo a ƙarshen makon da ya gabata kuma aka bar su su kula da kansu, in ji lauya Meredyth Yoon da ke zaune a Amurka a tattaunawarta da AFP.

Wani jirgi da zai iya ɗaukar mutum 14 ya isa Ghana tun daga lokacin, in ji Yoon, duk da cewa ba a bayyana adadin mutanen da ke cikin jirgin ba.

Ghana ta ce tana karɓar 'yan Yammacin Afirka ne bisa dalilai na jin kai kuma cewa yarjejeniyar ba ta zama wata “amincewa” da manufofin shige da fice na Amurka ba.