| hausa
AFIRKA
3 minti karatu
Amurka ta cire takunkumin biza kan Ghana bayan cim ma yarjejeniya kan karɓar waɗanda Trump ke kora
A farkon watan nan ne Shugaban Ghana John Dramani Mahama ya sanar da cewa ƙasarsa za ta rinƙa karɓar ‘yan Yammacin Afirka da Gwamnatin Trump ta kora.
Amurka ta cire takunkumin biza kan Ghana bayan cim ma yarjejeniya kan karɓar waɗanda Trump ke kora
“Takunkuman biza da Amurka ta ƙaƙaba wa Ghana” an “janye su,” in ji Ministan Harkokin Wajen Ghana, Samuel Okudzeto Ablakwa.
27 Satumba 2025

Amurka ta janye takunkumin biza da ta ƙaƙaba wa Ghana, in ji Ministan Harkokin Wajen Ghana a ranar Juma’a, yayin da ƙasar ta Yammacin Afirka ke zama cibiyar karɓar 'yan gudun hijira da aka kora a ƙarƙashin matakan hana shige da fice na Shugaba Donald Trump.

A farkon wannan watan, Shugaban Ghana John Mahama ya bayyana cewa ƙasar tana karɓar yammacin Afirka da aka kora daga Amurka.

Shugaba Donald Trump na Amurka ya sanya tsarin korar mutane zuwa ƙasashen da ba su da alaƙa da su ko ‘yan uwa a can a matsayin wani muhimmin ɓangare na manufofin hana shige da fice.

Duk da haka, Accra ta jaddada cewa ba ta samu wani abu a madadin karɓar waɗannan 'yan gudun hijirar ba, duk da cewa Mahama ya amince cewa an yi yarjejeniyar yayin da dangantaka ke ƙara tsanani, tare da Washington a daidai lokacin da take ƙaƙaba haraji da takunkumin biza a watannin baya-bayan nan.

“Takunkuman biza da Amurka ta ƙaƙaba wa Ghana” an “janye su,” in ji Ministan Harkokin Wajen Ghana, Samuel Okudzeto Ablakwa.

‘Labari mai dadi’

A cikin wani rubutu a X, Ablakwa ya bayyana cewa “labari mai dadi” ya fito ne daga jami’an Amurka a gefen taron Majalisar Dinkin Duniya. Ya ce wannan sauyin ya biyo bayan “watanni na tattaunawar diflomasiyya a matakin koli.”

A watan Yuni, Amurka ta sanar da takunkumin biza ga mafi yawan 'yan ƙasashen Kamaru, Habasha, Ghana da Nijeriya, inda aka takaita su zuwa watanni uku da izinin shiga sau ɗaya kawai.

“Yanzu 'yan Ghana za su iya samun biza ta tsawon shekaru biyar tare da damar shiga fiye da sau ɗaya tare da wasu fa'idojin ofishin jakadanci,” in ji Ablakwa.

Akalla mutum 14 daga Yammacin Afirka aka tura Ghana tun farkon watan Satumba, duk da cewa ba Accra ko Washington ba su bayyana cikakkun bayanai game da haka ba.

Dukkaninsu sun samu kariya daga kotunan shige da fice na Amurka kan korar su zuwa ƙasashensu na asali, in ji lauyoyinsu, duk da cewa Ghana ta tura aƙalla mutum huɗu zuwa ƙasashensu na asali, a cewar wata ƙididdigar AFP.

An tura su Togo

Bayan shafe makonnia tasare a Ghana, inda ake zargin suna tsare ne a ƙarƙashin kulawar sojoji kuma a cikin yanayi mara kyau, mutane takwas zuwa goma daga cikin waɗanda aka kora an tura su Togo a ƙarshen makon da ya gabata kuma aka bar su su kula da kansu, in ji lauya Meredyth Yoon da ke zaune a Amurka a tattaunawarta da AFP.

Wani jirgi da zai iya ɗaukar mutum 14 ya isa Ghana tun daga lokacin, in ji Yoon, duk da cewa ba a bayyana adadin mutanen da ke cikin jirgin ba.

Ghana ta ce tana karɓar 'yan Yammacin Afirka ne bisa dalilai na jin kai kuma cewa yarjejeniyar ba ta zama wata “amincewa” da manufofin shige da fice na Amurka ba.

Rumbun Labarai
Mahaucin Al Fasher: Yadda hotonsa ya zama alamar bakin cikin Sudan
UN Women: Mata da 'yan mata 11M suna fama da matsanancin ƙarancin abinci a Sudan sakamakon yaƙi
WHO ta bayyana damuwa kan karuwar masu ciwon siga a Afirka
Kisan kare dangi a boye da bayyane: Gushewar jinkai a Al Fasher
An ba da belin dan Gaddafi bayan da ya shafe shekaru 10 a tsare a Lebanon
Gwamnatin Trump 'ta aika wa Equatorial Guinea dala miliyan 7.5' don ta karɓi waɗanda Amurka ta kora
Ƙasashe fiye da 20 sun yi Allah wadai da RSF kan kashe-kashen da take yi a Sudan
Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya ya yi kira da a dakatar da zubar da jini a Sudan
Paul Biya na Kamaru: Dan siyasar da zai ci gaba da yin mulki har sai ya kai shekara 99?
Hare-haren RSF sun kori ƙarin dubban mutane daga Darfur da Kordofan na Sudan
RSF ta binne gawawwaki a kabarin bai-ɗaya, ta ƙone wasu domin 'ɓoye laifukan yaƙi': Likitocin Sudan
Sojojin Sudan sun harbo jirgi maras matuƙi na RSF a Kordofan ta Arewa
Dakarun Nijar sun cafke muggan makamai da aka yi safararsu daga Libya, sun kama masu safarar ƙwayoyi
RSF ta Sudan ta kai hare-hare a Jihar Khartoum da birnin Atbara bayan amincewa da tsagaita wuta
Paul Biya na Kamaru: Shugaban da ya fi tsufa a duniya ya sha rantsuwar kama aiki karo na takwas
Hatsarin mota ya yi ajalin fiye da mutum 1,000 a Nijar a shekarar 2023, fiye da 12,000 sun jikkata
Sabbin hotunan tauraron dan'adam sun gano alamun 'kaburburan bai-daya a El-Fasher a Sudan
MDD ta yi gargaɗin cewa yaƙin Sudan na gurgunta tattalin arzikin Sudan ta Kudu
Trump ya ce bai kamata Afirka ta Kudu ta kasance cikin G20 ba, ba zai je taronta a Johannesburg ba
'Yan Sudan sun ba da mummunan labarin yi wa mata fyade yayin da suke tserewa daga Al Fasher