| hausa
DUNIYA
2 minti karatu
UNGA 80: Trump ya yi alkawarin hana Isra'ila shirin ƙwace Yammacin Kogin Jordan
Shugabannin Ƙasashen Musulmai sun matsa wa Trump lamba kan ya yi gaggawar goyon bayan samar da tsagaita wuta a Gaza, da shigar da tallafi da samar da tsarin 'yancin kan Falasɗinu, suna gargadin samun tashin hankali a yankin in aka ci gaba da yaƙin.
UNGA 80: Trump ya yi alkawarin hana Isra'ila shirin ƙwace Yammacin Kogin Jordan
Shugabannin Musulmi na buƙatar dakatar da yaƙi nan take.
24 Satumba 2025

Shugaban Amurka Donald Trump ya tabbatar wa shugabannin Musulmi cewa ba zai bari Isra'ila ta ƙwace yankin Yammacin Kogin Jordan da aka mamaye ba, kamar yadda jaridar Politico ta ruwaito a ranar Laraba, tana ambaton mutane shida da suka san batun.

Trump ya yi wannan alkawari ne a yayin wani taro na sirri da aka gudanar a gefen babban taron Majalisar Dinkin Duniya a birnin New York, inda shugabannin Larabawa da Musulmi suka matsa wa Washington lamba kan ta mayar da hankali wajen kawo karshen yakin Isra'ila a Gaza.

A cewar jaridar Politico, ma’aikatan Trump sun rarraba wata takarda mai bayyana shirin gwamnatinsa na dakatar da rikicin, wanda ya hada da alkawarin hana mamaye yankin.

Taron, wanda aka shirya tare da goyon bayan Sarkin Qatar Sheikh Tamim bin Hamad Al Thani, ya hada shugabannin kasashe kamar na Turkiyya Recep Tayyip Erdogan, Sarkin Jordan Abdullah II, Shugaban Indonesia Prabowo Subianto, Firaministan Pakistan Shehbaz Sharif, Firaministan Masar Mostafa Madbouly, Ministan Harkokin Wajen Hadaddiyar Daular Larabawa Sheikh Abdullah bin Zayed Al Nahyan, da Ministan Harkokin Wajen Saudiyya Yarima Faisal bin Farhan.

‘Samar da zaman lafiya mai ɗorewa da adalci’

A cikin wata sanarwa ta hadin gwiwa da Riyadh ta fitar, shugabannin sun bayyana cewa kawo karshen yakin Gaza shi ne “mataki na farko wajen samar da zaman lafiya mai ɗorewa da adalci.”

Sun gargadi duniya kan “mummunan bala’in jinƙai” da kuma yawan mutanen farar hula da suka rasa rayukansu, inda hukumomin lafiya na Gaza suka ruwaito cewa sama da Falasdinawa 65,000 ne suka mutu tun watan Oktoban 2023.

Sun yi watsi da duk wani yunkuri na tilasta wa Falasdinawa barin gidajensu, tare da bukatar tsagaita wuta nan take wanda zai ba da damar dawowar wadanda aka raba da gidajensu, da kuma isar da tallafin jinƙai ba tare da wani cikas ba.

Haka kuma, sun bukaci samar da wata hanya ta tabbatar da kwanciyar hankali a yankin Yammacin Kogin Jordan da wuraren ibada masu tsarki na Birnin Kudus da gyare-gyare a cikin Hukumar Falasdinawa, da kuma wani shirin sake gina Gaza gaba daya karkashin jagorancin Larabawa da Ƙungiyar Haɗin Kan Ƙasashen Musulmi, OIC.

Masu bincike na Majalisar Dinkin Duniya kwanan nan sun kammala cewa Isra'ila tana aikata kisan kare dangi a Gaza, inda yawancin yankin ke fuskantar yunwa da bala’i da aka haddasa bayan shekaru na hare-hare.

Rumbun Labarai
COP30: Manyan masu gurbata muhalli na duniya ba su je taron sauyin yanayi na Brazil ba
Rasha ta ce tana sa ido kan Nijeriya bayan barazanar da Trump ya yi ta kai hari kasar
Zohran Mamdani: Matashi Musulmi na farko ya lashe zaɓen Magajin Birnin New York
Yadda amfani da magungunan antibiotic barkatai ya sa cututtuka suka zama makamai
Rundunar Sojin Ruwan Pakistan ta kama mugwayen ƙwayoyi na dala biliyan ɗaya a Tekun Arebiya
An gano sauro a karon farko a ƙasar Iceland
Yadda hukumomi a India suke farautar Musulmai da suke cewa 'Ina son Annabi Muhammad'
Putin ya gargaɗi Trump cewa bai wa Ukraine makamai mai linzamin Tomahawk zai jawo matsala tsakaninsu
Abin da muka sani game da mummunar arangamar kan iyaka tsakanin sojin Pakistan da Afganistan
Waiwayen 1903: An taɓa yi wa Yahudawa tayin Afirka, kamar yadda ake so a mayar da Falasɗinawa yanzu
An naɗa Sarah Mullally mace ta farko Shugabar Cocin Ingila
Yadda mutuwar ɓauna a turmutsutsu ke sauya salon farautar manyan namun dawa
An tsinci gawar jakadan Afirka ta Kudu a Faransa a wajen otal a birnin Paris
Babban Alkalin Kotun Amurka ya dakatar da umarnin Trump na korar ma’aikatan VOA
UNGA: Yadda ta kaya a taron 'nuna wa juna yatsa da huce haushi' na Majalisar Dinkin Duniya
Yadda jami'an diflomasiyyar duniya suka fice daga Zauren UNGA yayin da Netanyahu zai yi jawabi
Jawabin Trump a taron MDD ya fito da sakamakon nuna ƙyamar Musulunci a duniya
An yanke wa tsohon Shugaban Faransa Sarkozy hukuncin shekara biyar a gidan yari
Ga manyan batutuwa huɗu daga jawabin Sarkin Qatar a taron UNGA
Muradun Ƙungiyar G7 a UNGA sun haɗa da ƙara tallafa wa Ukraine da neman tsagaita wuta a Gaza