| hausa
GABAS TA TSAKIYA
1 minti karatu
MDD ta sake ƙaƙaba wa Iran sabbin takunkumai bayan kasa cim ma matsaya a tattaunawar nukiliya
Ƙasashen Faransa, Birtaniya da Jamus sun gargaɗi Iran kan cewa kada ta kuskura ta ɗauki wani mataki bayan saka mata waɗannan takunkuman, inda ƙasashen suka kuma ce saka takunkuman ba yana nufin ƙarshen tattaunawar diflomasiyya ba kenan.
MDD ta sake ƙaƙaba wa Iran sabbin takunkumai bayan kasa cim ma matsaya a tattaunawar nukiliya
Iran ta musanta zargin cewa tana neman ƙera makamin nukiliya.
28 Satumba 2025

Majalisar Dinkin Duniya ta sake ƙaƙaba wa Iran takunkumai bayan kasa cim ma matsaya a tattaunawar ƙarshe kan shirin nukiliyarta, inda Faransa, Birtaniya da Jamus suka gargaɗi Tehran kan ɗaukar matakan da za su kara dagula lamarin.

"Sake kakaba takunkuman Majalisar Dinkin Duniya ba yana nufin ƙarshen diflomasiyya ba ne," in ji ministocin harkokin wajen ƙasashen uku na Turai, da aka fi sani da E3, a cikin wata sanarwa ta haɗin gwiwa a ranar Lahadi.

"Muna kira ga Iran da ta guji ɗaukar matakan da za su ƙara dagula lamarin, sannan ta koma bin ƙa'idojin da suka zama dole a ƙarƙashin yarjejeniyoyin tsaron da suka shafi doka," kamar yadda suka ƙara da cewa.

Sake ƙaƙaba wa Iran takunkuman ya samo asali ne daga matakin da ƙasashen uku suka ɗauka a Kwamitin Tsaro na Majalisar Ɗinkin Duniya (Jamus ta hanyar sauran biyun), bisa zargin cewa ƙasar ta karya yarjejeniyar 2015 da aka tsara domin hana ta samar da makamin nukiliya.

Iran ta musanta zargin cewa tana neman ƙera makamin nukiliya.

Rumbun Labarai
Sau 27 Yahudawa 'yan-kama-wuri-zauna suka kutsa Masallacin Kudus a watan da ya wuce - Falasdinu
Bayanai na hukuma sun nuna cewa sojojin Isra'ila sun yi yunkurin kashe kansu sau 279 cikin wata 18
Hare-haren Isra'ila a Gaza sun kashe mutane 91, ciki har da yara 24, duk da tsagaita wuta
Netanyahu ya ba da umarnin a kai 'hare-hare masu karfi' kan Gaza
Shin Trump zai yanke alaka da Isra'ila idan ta ci gaba da mamaye Gabar Yammacin Kogin Jordan?
Amurka ta tsare ɗan jaridar Birtaniya Musulmi mai suna Sami Hamdi saboda sukar Isra'ila
Fiye da tan miliyan 61 na tarkace da baraguzai sun rufe Gaza a shekara biyu na yakin Isra'ila: UNRWA
Kalaman Trump na lalata cibiyoyin nukiliyar Iran 'mafarki ne': Khamenei
Wata ƙungiyar bayar da agaji ta Turkiyya ta ƙaddamar aikin kwashe ɓaraguzai a arewacin Gaza
Sojojin Israila sun buɗe wuta kan wasu manoma Falasɗinawa a yayin da suke girbe zaitun a Gaɓar Yamma
Mene ne abu na gaba a shirin zaman lafiya na Gaza?
Isra'ila ta sake buɗe mashigar Rafah don bai wa manyan motocin kayan agaji damar shiga Gaza
Turkiyya, Masar, Qatar da Amurka sun sa hannu kan takardar yarjejeniyar tsagaita wuta ta Gaza
Dauwamammen zaman lafiya zai samu ne kawai ta hanyar kafa ƙasashe biyu, Erdogan ya faɗa wa Starmer
Sojojin Hamas sun kashe mutum 32 cikin 'gungun' da ke sace kayan agaji a Gaza
Hamas ta kammala sakin 'yan Isra'ila 20 da ta tsare a matakin farko na yarjejeniyar tsagaita wuta
Wani bidiyo ya nuna yadda Isra'ila ke cin zarafin fursunonin Falasɗinawa gabanin sakin su
Trump, Sisi za su jagoranci taron zaman lafiya kan Gaza a birnin Sharm el-Sheikh a ranar Litinin
Sojojin Amurka sun isa Isra'ila domin sa ido kan aiwatar da yarjejeniyar tsagaita wuta ta Gaza
Sojojin Isra'ila sun fara janyewa a hankali zuwa gabashin Gaza: Kafofin watsa labarai